< Mattiyu 18 >
1 A lokacin nan sai almajirai suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Wane ne mafi girma a mulkin sama?”
I den samme Stund kom Disciplene hen til Jesus og sagde: „Hvem er da den største i Himmeriges Rige?”
2 Sai ya kira ƙaramin yaro ya sa shi yă tsaya a tsakiyarsu.
Og han kaldte et lille Barn til sig og stillede det midt iblandt dem
3 Sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in ba kun canja kuka zama kamar ƙananan yara ba, labudda, ba za ku shiga mulkin sama ba.
og sagde: „Sandelig, siger jeg eder, uden I omvende eder og blive som Børn, komme I ingenlunde ind i Himmeriges Rige.
4 Saboda haka, duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar wannan yaro, shi ne mafi girma a mulkin sama.
Derfor, den, som fornedrer sig selv som dette Barn, han er den største i Himmeriges Rige.
5 Duk kuma wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan a cikin sunana ya karɓe ni ne.
Og den, som modtager et eneste saadant Barn for mit Navns Skyld, modtager mig.
6 “Amma duk wanda ya sa ɗaya daga cikin ƙananan nan da suka gaskata da ni ya yi zunubi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.
Men den, som forarger een af disse smaa, som tro paa mig, ham var det bedre, at der var hængt en Møllesten om hans Hals, og han var sænket i Havets Dyb.
7 Kaiton duniya saboda abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi! Dole irin waɗannan abubuwa su zo, sai dai kaiton mutumin da ya zama sanadin kawo su!
Ve Verden for Forargelserne! Thi vel er det nødvendigt, at Forargelserne komme; dog, ve det Menneske, ved hvem Forargelsen kommer!
8 In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios )
Men dersom din Haand eller din Fod forarger dig, da hug den af, og kast den fra dig! Det er bedre for dig at gaa lam eller som en Krøbling ind til Livet end at have to Hænder og to Fødder og blive kastet i den evige Ild. (aiōnios )
9 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna )
Og dersom dit Øje forarger dig, da riv det ud, og kast det fra dig! Det er bedre for dig at gaa enøjet ind til Livet end at have to Øjne og blive kastet i Helvedes Ild. (Geenna )
10 “Ku lura, kada ku rena ɗaya daga cikin waɗannan ƙanana. Gama ina faɗa muku mala’ikunsu a sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin sama.
Ser til, at I ikke foragte en eneste af disse smaa; thi jeg siger eder: Deres Engle i Himlene se altid min Faders Ansigt, som er i Himlene.
[Thi Menneskesønnen er kommen for at frelse det fortabte.]
12 “Me kuka gani? In wani yana da tumaki ɗari, sai ɗaya daga cikinsu ta ɓace, ba sai yă bar tasa’in da taran a kan tuddai yă je neman guda ɗayan da ta ɓace ba?
Hvad tykkes eder? Om et Menneske har hundrede Faar, og eet af dem farer vild, forlader han da ikke de ni og halvfemsindstyve og gaar ud i Bjergene og leder efter det vildfarende?
13 In kuwa ya same ta, ina gaya muku gaskiya, zai yi murna saboda ɗayan fiye da tasa’in da taran da ba su ɓace ba.
Og hænder det sig, at han finder det, sandelig, siger jeg eder, han glæder sig mere over det end over de ni og halvfemsindstyve, som ikke ere farne vild.
14 Haka ma Ubanku da yake cikin sama ba ya so ko ɗaya daga cikin ƙananan nan yă ɓace.
Saaledes er det ikke eders himmelske Faders Villie, at en eneste af disse smaa skal fortabes.
15 “In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, ka je ka nuna masa laifinsa, tsakaninku biyu kaɗai. In ya saurare ka, ka maido da ɗan’uwanka ke nan.
Men om din Broder synder imod dig, da gaa hen og revs ham mellem dig og ham alene; hører han dig, da har du vundet din Broder.
16 Amma in bai saurare ka ba, ka je tare da mutum ɗaya ko biyu, domin ‘a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.’
Men hører han dig ikke, da tag endnu en eller to med dig, for at „hver Sag maa staa fast efter to eller tre Vidners Mund.”
17 In kuwa ya ƙi yă saurare su, sai ka gaya wa ikkilisiya; in kuma ya ƙi yă saurari ikkilisiya ma, ka yi da shi kamar marar sanin Allah ko mai karɓar haraji.
Men er han dem overhørig, da sig det til Menigheden; men er han ogsaa Menigheden overhørig, da skal han være for dig ligesom en Hedning og en Tolder.
18 “Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka daure a duniya, za a daure a sama, duk kuma abin da kuka kunce a duniya, za a kunce shi a sama.
Sandelig, siger jeg eder, hvad som helst I binde paa Jorden, skal være bundet i Himmelen; og hvad som helst I løse paa Jorden, skal være løst i Himmelen.
19 “Har wa yau, ina gaya muku cewa in mutum biyu a cikinku a duniya suka yarda su roƙi wani abu, Ubana da yake cikin sama zai yi muku.
Atter siger jeg eder, at dersom to af eder blive enige paa Jorden om hvilken som helst Sag, hvorom de ville bede, da skal det blive dem til Del fra min Fader, som er i Himlene.
20 Gama inda mutum biyu ko uku suka taru cikin sunana, a can ma ina tare da su.”
Thi hvor to eller tre ere forsamlede om mit Navn, der er jeg midt iblandt dem.”
21 Sai Bitrus ya zo wurin Yesu ya yi masa tambaya ya ce, “Ubangiji, sau nawa zan yafe wa ɗan’uwana sa’ad da ya yi mini zunubi? Har sau bakwai?”
Da traadte Peter frem og sagde til ham: „Herre! hvor ofte skal jeg tilgive min Broder, naar han synder imod mig? mon indtil syv Gange?”
22 Yesu amsa ya ce, “Ina gaya maka, ba sau bakwai ba, amma sau saba’in da bakwai.
Jesus siger til ham: „Jeg siger dig: ikke indtil syv Gange, men indtil halvfjerdsindstyve Gange syv Gange.
23 “Saboda haka, mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya so yă yi ƙididdigar dukiyarsa da take a hannun bayinsa.
Derfor lignes Himmeriges Rige ved en Konge, som vilde holde Regnskab med sine Tjenere.
24 Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wani wanda yake bin bashin talenti dubu goma.
Men da han begyndte at holde Regnskab, blev en, som var ti Tusinde Talenter skyldig, ført frem for ham.
25 Da yake bai iya biya ba, sai maigida ya umarta a sayar da shi da matarsa da yaransa da kuma duk abin da yake da shi, a biya bashin.
Og da han intet havde at betale med, bød hans Herre, at han og hans Hustru og Børn og alt det, han havde, skulde sælges, og Gælden betales.
26 “Bawan ya durƙusa a gabansa. Ya yi roƙo ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka ƙaf.’
Da faldt Tjeneren ned for ham, bønfaldt ham og sagde: Herre, vær langmodig med mig, saa vil jeg betale dig det alt sammen.
27 Maigidan bawan ya ji tausayinsa, ya yafe masa bashin, ya kuma sake shi.
Da ynkedes samme Tjeners Herre inderligt over ham og lod ham løs og eftergav ham Gælden.
28 “Amma da wannan bawa ya fita, sai ya gamu da wani abokin bautarsa wanda yake binsa bashin dinari ɗari. Sai ya cafke shi, ya shaƙe shi a wuya yana cewa, ‘Biya ni abin da nake binka!’
Men den samme Tjener gik ud og traf en af sine Medtjenere, som var ham hundrede Denarer skyldig; og han greb fat paa ham og var ved at kvæle ham og sagde: Betal, hvad du er skyldig!
29 “Wannan abokin bautarsa ya durƙusa ya roƙe shi, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka.’
Da faldt hans Medtjener ned for ham og bad ham og sagde: Vær langmodig med mig, saa vil jeg betale dig.
30 “Amma ya ƙi. A maimako, sai ya je ya sa aka jefa shi a kurkuku, har yă biya bashin.
Men han vilde ikke, men gik hen og kastede ham i Fængsel, indtil han betalte, hvad han var skyldig.
31 Sa’ad da sauran bayin suka ga abin da ya faru, abin ya ɓata musu rai ƙwarai, sai suka tafi suka faɗa wa maigidansu dukan abin da ya faru.
Da nu hans Medtjenere saa det, som skete, bleve de saare bedrøvede og kom og forklarede for deres Herre alt, hvad der var sket.
32 “Sai maigidan ya kira wannan bawa. Ya ce, ‘Kai mugun bawa, na yafe duk bashin da nake binka domin ka roƙe ni.
Da kalder hans Herre ham for sig og siger til ham: Du onde Tjener! al den Gæld eftergav jeg dig, fordi du bad mig.
33 Ashe, bai kamata kai ma ka ji tausayin abokin bautarka yadda na yi maka ba?’
Burde ikke ogsaa du forbarme dig over din Medtjener, ligesom jeg har forbarmet mig over dig.
34 Cikin fushi, maigidan ya miƙa shi ga ma’aikatan kurkuku su gwada masa azaba, har yă biya dukan bashin da ake binsa.
Og hans Herre blev vred og overgav ham til Bødlerne, indtil han kunde faa betalt alt det, han var ham skyldig.
35 “Haka Ubana da yake cikin sama zai yi da kowannenku, in ba ku yafe wa’yan’uwanku daga zuciyarku ba.”
Saaledes skal ogsaa min himmelske Fader gøre mod eder, om I ikke af Hjertet tilgive, enhver sin Broder.”