< Mattiyu 17 >
1 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
Sa arok lini Jisu ih heh damdi Pitar nyia soophoh wanyi Jeems nyia Joon loong ah hatik ko ih neng luulu kongchoong ni siitwan rumta.
2 A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
Neng miksok di, Jisu ah maama ih lekta: hethe hekhoh ah rangsa likhiik ih phaakta, eno henyuh hekhat ah pungkoopkoop ih phaakta.
3 Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
Erah lidi heliphante wajom ah ih Jisu ah Moses nyia Elija damdi waan arah tup rumta.
4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Eno Pitar ih Jisu suh baatta, “Teesu, tumthan jaase ah seng aani roong ang heeno ah! An thungpun ubah, ngah ih nyutaap arah doh ejom than hoon ang joh, esiit ah an raangtaan ih, esiit ah Moses raangtaan ih eno esiit ah Elija raangtaan ih ah.”
5 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
Heh waan tokdi, jiingmuung ah phaakjaaja ih heh khothung ni ra taha, eno jiingmuung mong adi root dongjengta, “Arah nga mongnook amiisak nga Sah, heh suh Ngah eroon elang—heh jeng ah boichaat et an!”
6 Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
Heliphante loong ah ih erah jeng ah japchaat rum ano rapne ih cho rumta eno hah ni pheengbon rumta.
7 Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
Jisu ah neng reeni ra haano taajoh rumta. “Saat an,” heh ih liita. “Nakcho an!”
8 Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
Eno toonsok rum adi heh damdi o uh tajeeta Jisu luulu angta.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
Neng kong nawa dat ra rumha di, Jisu ih baat rumta, o suh uh labaat theng marah sen ih mot amang ni japtup tan rah ah, Mina Sah ah tek nawa maang ngaaksaatka ngakhoh nah ah.
10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
Eno heliphante loong ih Jisu suh cheng rumta, “Hootthe nyootte loong ah ih Elija ah jaakhoh raaha ih mamet baat rumta?”
11 Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
“Jaakhoh Elija aju raaha,” Jisu ih liita, “Eno heh ih jaatrep ban khookham raaha.
12 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
Enoothong ngah ih baat rumhala, Elija abah ejen raak ih taha, mina loong ih ba heh ah tajen samjat rumka, heh damdi emungmaang ih reeraang rumla. Erah likhiik Mina Sah rah uh emamah et joonnaam rum ah.”
13 Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
Eno heliphante loong ah ih Juungtemte Joon tiit boh baat ha ih dongjat rumta.
14 Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
Neng miloong dung ni ngaak wang rum adi, wasiit Jisu ngathong ni heh lakudi tongwang ano
15 Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
liita, “Chuupha, nga sah ah minchan weeuh! Heh ah wakngak angla, baphuk ih we nyia juung ni choophaan phaan bondat leh mangtek kah eah.
16 Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
Ngah ih an liphante loong jiinni taatsiit jatahang, ang abah uh neng ih tajen deesiit rumta.”
17 Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
Jisu ih ngaakbaat rumta, “Mina sen loong ah mamah lahanpi elan nyia moongtaang lan! Ngah sen damdam sa mathan ma jen roong tonghang nyia roong reehang? Noodek ah nga jiinko ih siitwan han!”
18 Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
Jisu ih laathih ah kanjaata, eno noodek sak dowa laathih ah doksoon kata, eno erah radi noodek ah laan de ruh eta.
19 Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
Eno heliphante loong ah Jisu suh husah ih cheng rumta, “Laathih ah seng ih mamah lajen dokphan etti?”
20 Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
“Erah langla sendi tuungmaang ah ehan laje kokan no,” Jisu ih ngaakbaat rumta. “Ngah ih amiimi baat rumhala sen tuungmaang ah miinjaangjih thanthan je bah, sen ih arah kong akaan asuh botseh ejen baat et an, ‘Arah dowa therah ko ih kah uh eah!’ Eno amiimiisak ih kah ah. Sen ih tumjih uh ejen re ean!”
Enoothong arah likhiik ah rangsoom nyia samurangsoom lam ih ba jen dokphan an; jaat hoh tumjih nawa re uh tajenka.
22 Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
Heliphante loong Galili ni lomkhoom rumha di, Jisu ih baat rumta, “Mina Sah ah mih lak nah kot suh saapoot chang ela
23 Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
eno heh ah tek haat et rum ah; enoothong sa jom lih doh ewe engaakthing eah.” Heliphante loong ah rapne ih thungthih rumta.
24 Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
Jisu nyia heliphante loong Kapernum hadaang ni thokrum adi, Rangteenok thaang sokseete loong Pitar jiinni wang haano cheng rumta, “Sen suh nyootte warah ih Rangteenok sokse ah ekot nikah et ah?”
25 Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
“Ekot kah et ah,” Pitar ih ngaakbaatta. Pitar ah nokmong ni wang adi, Jisu ih heh suh phang chengta, “Simoon, an ih tumjih thunhu? Arah mongrep dowa luungwang loong asuh lakbi thaang nyia sokse ah o ih kakoh ah? Heh deek akaan nawa ih tamkoh ah tama mideek nawa ih koh ah?”
26 Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
“Mihate ih koh ah,” Pitar ih ngaakbaatta. “Jisu ih liita, ese,” “Erah langla hanok ih bah lakotjih boh ah.
27 Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”
Enoothong seng ih arah loong ah emoong tahoon thuk ke. Erah raang ih juungsitum adoh riitchap kah anno nyathan than kah an. Eno marah jaakhothoon nyaan ah, erah nyah tui adoh jaan ngun choh an eno erah seng sokse kotheng laaleh ang ah. Erah pi anno sokse ah kokaat an.”