< Mattiyu 17 >
1 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
Un pēc sešām dienām Jēzus ņēma Pēteri un Jēkabu un šā brāli, Jāni, un tos veda savrup uz augstu kalnu,
2 A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
Un tapa apskaidrots viņu priekšā, un Viņa vaigs spīdēja kā saule, un Viņa drēbes tapa baltas kā gaisma.
3 Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
Un redzi, Mozus un Elija tiem parādījās un runāja ar Viņu.
4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Un Pēteris vērsās pie Jēzus un sacīja: “Kungs, šeit mums labi! Ja Tu gribi, tad mēs šeitan trīs būdas taisīsim, vienu Tev, vienu Mozum, un vienu Elijam.”
5 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
Tam vēl runājot, redzi, spožs padebesis tos apēnoja, un redzi, balss no tā padebeša sacīja: “Šis ir Mans mīļais Dēls, pie kā Man ir labs prāts, To jums būs klausīt.”
6 Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
Kad tie mācekļi to dzirdēja, tad tie krita uz savu vaigu un izbijās ļoti.
7 Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
Bet Jēzus nāca, tos aizskāra un sacīja: “Ceļaties un nebīstaties.”
8 Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
Bet kad tie savas acis pacēla, tad tie neredzēja nevienu kā tik vien Jēzu.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
Un no kalna noejot, Jēzus tiem pavēlēja un sacīja: “Nesakiet nevienam šo parādīšanos, tiekams Tas Cilvēka Dēls nebūs uzcēlies no miroņiem.”
10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
Un Viņa mācekļi Viņam vaicāja sacīdami: “Ko tad tie rakstu mācītāji saka, ka Elijam jānāk papriekš?”
11 Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
Bet Jēzus atbildēja un uz tiem sacīja: “Elija gan nāk papriekš un visu atkal sataisīs.
12 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
Bet Es jums saku, ka Elija jau ir nācis, tomēr tie viņu nav atzinuši, bet ar viņu darījuši, ko gribēdami. Tā arī Tam Cilvēka Dēlam būs jācieš no viņiem.”
13 Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
Tad tie mācekļi saprata, ka Viņš tiem sacījis no Jāņa, tā Kristītāja.
14 Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
Un kad tie nāca pie tiem ļaudīm, tad viens cilvēks pie Viņa atnāca un metās ceļos Viņa priekšā
15 Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
Un sacīja: “Kungs, apžēlojies par manu dēlu, jo viņš ir mēnessērdzīgs un viņam briesmīgi jācieš; jo dažkārt viņš krīt ugunī un dažkārt ūdenī.
16 Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
Un es to pie Taviem mācekļiem esmu atvedis, bet tie to nevarēja veselu darīt.”
17 Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
Bet Jēzus atbildēja un sacīja: “Ak tu neticīgā un netiklā cilts, cik ilgi Es vēl būšu pie jums? Cik ilgi Es jūs panesīšu? Vediet Man viņu šurp.”
18 Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
Un Jēzus viņu apdraudēja, un velns no viņa izbēga; un tas zēns palika vesels tanī pašā stundā.
19 Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
Tad tie mācekļi piegāja pie Jēzus atsevišķi un sacīja: “Kāpēc mēs viņu nevarējām izdzīt?”
20 Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
Un Jēzus uz tiem sacīja: “Jūsu neticības dēļ; jo patiesi, Es jums saku: kad jums ticība ir kā sinepju graudiņš, tad jūs sacīsiet šim kalnam: nocelies no šejienes uz turieni, un viņš nocelsies, un nekas jums nebūs neiespējams.
Bet šī suga neizbēg kā vien caur lūgšanu un gavēšanu.”
22 Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
Kad nu tie Galilejā apkārt staigāja, tad Jēzus uz tiem sacīja: “Tas Cilvēka Dēls taps nodots cilvēku rokās.
23 Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
Un Viņu nokaus, un trešā dienā Viņš celsies augšām;” un tie ļoti noskuma.
24 Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
Un kad tie Kapernaūmā nāca, tad tie nodokļu saņēmēji atnāca pie Pētera un sacīja: “Vai jūsu Mācītājs nodokli nedod?”
25 Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
Viņš sacīja: “Dod gan.” Un kad tas namā bija iegājis, Jēzus viņam papriekš vaicāja sacīdams: “Ko tu domā, Sīman? No kuriem laicīgie ķēniņi ņem muitu un nodokli? Vai no saviem bērniem, vai no svešiniekiem?”
26 Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
Pēteris uz Viņu sacīja: “No svešiniekiem.” Tad Jēzus uz to sacīja: “Tad tie bērni ir svabadi.
27 Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”
Bet lai mēs tiem nedodam apgrēcību, tad ej jūrmalā un izmet makšķeri, un to pirmo zivi, kas piekodīsies, ņem, un viņas muti atdarījis, tu atradīsi vienu stateri, to ņem un dod viņiem priekš Manis un tevis.”