< Mattiyu 17 >

1 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
Et après six jours, Jésus prend avec lui Pierre, et Jacques, et Jean son frère, et les mène à l’écart sur une haute montagne.
2 A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
Et il fut transfiguré devant eux; et son visage resplendit comme le soleil, et ses vêtements devinrent blancs comme la lumière.
3 Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
Et voici, Moïse et Élie leur apparurent, parlant avec lui.
4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Et Pierre, répondant, dit à Jésus: Seigneur, il est bon que nous soyons ici; si tu le veux, faisons ici trois tentes: une pour toi, et une pour Moïse, et une pour Élie.
5 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
Comme il parlait encore, voici, une nuée lumineuse les couvrit; et voici une voix de la nuée, disant: Celui-ci est mon fils bien-aimé, en qui j’ai trouvé mon plaisir; écoutez-le.
6 Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
Ce que les disciples ayant entendu, ils tombèrent le visage contre terre et furent saisis d’une très grande peur.
7 Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
Et Jésus, s’approchant, les toucha et dit: Levez-vous, et n’ayez point de peur.
8 Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
Et eux, levant leurs yeux, ne virent personne que Jésus seul.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
Et comme ils descendaient de la montagne, Jésus leur enjoignit, disant: Ne dites à personne la vision, jusqu’à ce que le fils de l’homme soit ressuscité d’entre les morts.
10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
Et ses disciples l’interrogèrent, disant: Pourquoi donc les scribes disent-ils qu’il faut qu’Élie vienne premièrement?
11 Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
Et lui, répondant, leur dit: En effet, Élie vient premièrement, et il rétablira toutes choses;
12 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
mais je vous dis qu’Élie est déjà venu, et ils ne l’ont pas reconnu; mais ils lui ont fait tout ce qu’ils ont voulu; ainsi aussi le fils de l’homme va souffrir de leur part.
13 Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
Alors les disciples comprirent qu’il leur parlait de Jean le baptiseur.
14 Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
Et quand ils furent venus auprès de la foule, un homme s’approcha de lui, se jetant à genoux devant lui,
15 Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
et disant: Seigneur, aie pitié de mon fils, car il est lunatique et souffre cruellement, car souvent il tombe dans le feu, et souvent dans l’eau;
16 Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
et je l’ai apporté à tes disciples, et ils n’ont pu le guérir.
17 Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
Et Jésus, répondant, dit: Ô génération incrédule et perverse, jusques à quand serai-je avec vous; jusques à quand vous supporterai-je? Amenez-le-moi ici.
18 Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
Et Jésus le tança; et le démon sortit de lui; et le jeune garçon fut guéri dès cette heure-là.
19 Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
Alors les disciples, venant à Jésus à l’écart, dirent: Pourquoi n’avons-nous pu le chasser?
20 Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
Et Jésus leur dit: À cause de votre incrédulité; car, en vérité, je vous dis: si vous aviez de la foi comme un grain de moutarde, vous diriez à cette montagne: Transporte-toi d’ici là, et elle se transporterait; et rien ne vous serait impossible.
Mais cette sorte ne sort que par la prière et par le jeûne.
22 Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
Et comme ils séjournaient en Galilée, Jésus leur dit: Le fils de l’homme va être livré entre les mains des hommes;
23 Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
et ils le feront mourir; et le troisième jour il sera ressuscité. Et ils furent fort attristés.
24 Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
Et lorsqu’ils furent venus à Capernaüm, les receveurs des didrachmes vinrent à Pierre, et dirent: Votre maître ne paie-t-il pas les didrachmes?
25 Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
Il dit: Oui. Et quand il fut entré dans la maison, Jésus le prévint, disant: Que t’en semble, Simon? Les rois de la terre, de qui reçoivent-ils des tributs ou des impôts, de leurs fils ou des étrangers?
26 Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
Pierre lui dit: Des étrangers. Jésus lui dit: Les fils en sont donc exempts.
27 Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”
Mais, afin que nous ne les scandalisions pas, va-t’en à la mer, jette un hameçon, et prends le premier poisson qui montera; et quand tu lui auras ouvert la bouche, tu y trouveras un statère; prends-le, et donne-le-leur pour moi et pour toi.

< Mattiyu 17 >