< Mattiyu 17 >

1 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
And after six days, Jesus taketh Peter, and James, and John his brother, and bringeth them up to a high mountain apart;
2 A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
and was transfigured before them: and his face shone like the sun, and his raiment became white as the light.
3 Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
And they saw Moses and Elias talking with Him.
4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Then Peter said unto Jesus, Lord, it is good for us to be here: if thou pleasest, let us make three tabernacles here, one for Thee, and one for Moses, and one for Elias.
5 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
And as he was speaking, lo a bright cloud overshadowed them, and a voice out of the cloud, saying, This is my beloved Son, in whom I am well pleased; hear ye Him.
6 Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
And when the disciples heard it, they fell on their face, and were sore afraid.
7 Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
But Jesus came and touched them and said, Rise up and be not afraid.
8 Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
And when they lifted up their eyes, they saw none but Jesus only.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
And as they came down from the mountain, Jesus charged them, saying, Tell the vision to no one, till the Son of man be risen from the dead.
10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
And his disciples asked Him, saying, Why then do the scribes say, that Elias must first come?
11 Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
Jesus said unto them, Elias doth indeed come first, and shall set all things right.
12 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
But I tell you that Elias is come already, and they knew him not, but did what they pleased to him: and so is the Son of man to suffer by them.
13 Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
Then the disciples understood that He spake to them of John the baptist.
14 Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
And when they were come to the multitude, there came to Him a man kneeling down and saying,
15 Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
Lord, have compassion upon my son, for he is lunatic and grievously afflicted; for he often falleth into the fire, and often into the water.
16 Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
And I brought him to thy disciples, and they could not heal him.
17 Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
Then Jesus answered and said, O unbelieving and perverse generation, how long shall I be with you? how long shall I bear with you?
18 Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
Bring him here to me. And when Jesus rebuked him, the demon departed out of him, and the child was cured from that time.
19 Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
Then came the disciples to Jesus in private, and said, Why could not we cast him out?
20 Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
And Jesus said unto them, because of your unbelief: for verily I tell you, if ye had but faith as a grain of mustard-seed, ye might say to this mountain, Remove from hence thither, and it shall remove: and nothing would be impossible to you.
But this kind is not to be cast out but by prayer and fasting.
22 Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
And while they were in Galilee, Jesus said unto them, the Son of man is to be delivered into the hands of men:
23 Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
and they will put Him to death, and the third day He shall be raised again. And they were exceedingly grieved.
24 Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
And when they were come to Capernaum, the receivers of the tribute-money came to Peter and said, Doth not your master pay tribute? Yes, saith he.
25 Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
And when he came into the house, Jesus prevented him and said, What thinkest thou, Simon? Of whom do the kings of the earth take custom or tribute? Of their own children, or of other people?
26 Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
Peter saith unto Him, Of others. Jesus answered him, Then are the children free:
27 Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”
but that we may not give them offence, go to the sea-side and throw in a hook, and take the first fish that comes up, and open its mouth, and thou shalt find a piece of money: that take and give them for me and thee.

< Mattiyu 17 >