< Mattiyu 17 >

1 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
Six day later, Jesus took with Him Peter and the brothers James and John, and brought them up a high mountain to a solitary place.
2 A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
There in their presence His form underwent a change; His face shone like the sun, and His raiment became as white as the light.
3 Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
And suddenly Moses and Elijah appeared to them conversing with Him.
4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Then Peter said to Jesus, "Master, we are thankful to you that we are here. If you approve, I will put up three tents here, one for you, one for Moses, and one for Elijah."
5 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
He was still speaking when a luminous cloud spread over them; and a voice was heard from within the cloud, which said, "This is My Son dearly beloved, in whom is My delight. Listen to Him."
6 Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
On hearing this voice, the disciples fell on their faces and were filled with terror.
7 Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
But Jesus came and touched them, and said, "Rouse yourselves and have no fear."
8 Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
So they looked up, and saw no one but Jesus.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
As they were descending the mountain, Jesus laid a command upon them. "Tell no one," He said, "of the sight you have seen till the Son of Man has risen from among the dead."
10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
"Why then," asked the disciples, "do the Scribes say that Elijah must first come?"
11 Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
"Elijah was indeed to come," He replied, "and would reform everything.
12 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
But I tell you that he has already come, and they did not recognize him, but dealt with him as they chose. And before long the Son of Man will be treated by them in a similar way."
13 Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
Then it dawned upon the disciples that it was John the Baptist about whom He had spoken to them.
14 Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
When they had returned to the people, there came to Him a man who fell on his knees before Him and besought Him.
15 Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
"Sir," he said, "have pity on my son, for he is an epileptic and is very ill. Often he falls into the fire and often into the water.
16 Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
I have brought him to your disciples, and they have not been able to cure him."
17 Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
"O unbelieving and perverse generation!" replied Jesus; "how long shall I be with you? how long shall I endure you? Bring him to me."
18 Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
Then Jesus reprimanded the demon, and it came out and left him; and the boy was cured from that moment.
19 Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
Then the disciples came to Jesus privately and asked Him, "Why could not we expel the demon?"
20 Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
"Because your faith is so small," He replied; "for I solemnly declare to you that if you have faith like a mustard-seed, you shall say to this mountain, 'Remove from this place to that,' and it will remove; and nothing shall be impossible to you.
But an evil spirit of this kind is only driven out by prayer and fasting."
22 Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
As they were travelling about in Galilee, Jesus said to them, "The Son of Man is about to be betrayed into the hands of men;
23 Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
they will put Him to death, but on the third day He will be raised to life again." And they were exceedingly distressed.
24 Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
After their arrival at Capernaum the collectors of the half-shekel came and asked Peter, "Does not your Teacher pay the half-shekel?"
25 Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
"Yes," he replied, and then went into the house. But before he spoke a word Jesus said, "What think you, Simon? From whom do this world's kings receive customs or capitation tax? from their own children, or from others?"
26 Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
"From others," he replied. "Then the children go free," said Jesus.
27 Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”
"However, lest we cause them to sin, go and throw a hook into the Lake, and take the first fish that comes up. When you open its mouth, you will find a shekel in it: bring that coin and give it to them for yourself and me."

< Mattiyu 17 >