< Mattiyu 16 >
1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
tadAnIM phirUshinaH sidUkinashchAgatya taM parIkShituM nabhamIyaM ki nchana lakShma darshayituM tasmai nivedayAmAsuH|
2 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
tataH sa uktavAn, sandhyAyAM nabhaso raktatvAd yUyaM vadatha, shvo nirmmalaM dinaM bhaviShyati;
3 da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
prAtaHkAle cha nabhaso raktatvAt malinatvA ncha vadatha, jha nbhshadya bhaviShyati| he kapaTino yadi yUyam antarIkShasya lakShma boddhuM shaknutha, tarhi kAlasyaitasya lakShma kathaM boddhuM na shaknutha?
4 Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
etatkAlasya duShTo vyabhichArI cha vaMsho lakShma gaveShayati, kintu yUnaso bhaviShyadvAdino lakShma vinAnyat kimapi lakShma tAn na darshayiyyate| tadAnIM sa tAn vihAya pratasthe|
5 Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
anantaramanyapAragamanakAle tasya shiShyAH pUpamAnetuM vismR^itavantaH|
6 Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
yIshustAnavAdIt, yUyaM phirUshinAM sidUkinA ncha kiNvaM prati sAvadhAnAH satarkAshcha bhavata|
7 Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
tena te parasparaM vivichya kathayitumArebhire, vayaM pUpAnAnetuM vismR^itavanta etatkAraNAd iti kathayati|
8 Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
kintu yIshustadvij nAya tAnavochat, he stokavishvAsino yUyaM pUpAnAnayanamadhi kutaH parasparametad viviMkya?
9 Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
yuShmAbhiH kimadyApi na j nAyate? pa nchabhiH pUpaiH pa nchasahasrapuruSheShu bhojiteShu bhakShyochChiShTapUrNAn kati DalakAn samagR^ihlItaM;
10 Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
tathA saptabhiH pUpaishchatuHsahasrapuruSheShu bhejiteShu kati DalakAn samagR^ihlIta, tat kiM yuShmAbhirna smaryyate?
11 Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
tasmAt phirUshinAM sidUkinA ncha kiNvaM prati sAvadhAnAstiShThata, kathAmimAm ahaM pUpAnadhi nAkathayaM, etad yUyaM kuto na budhyadhve?
12 Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
tadAnIM pUpakiNvaM prati sAvadhAnAstiShThateti noktvA phirUshinAM sidUkinA ncha upadeshaM prati sAvadhAnAstiShThateti kathitavAn, iti tairabodhi|
13 Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
apara ncha yIshuH kaisariyA-philipipradeshamAgatya shiShyAn apR^ichChat, yo. ahaM manujasutaH so. ahaM kaH? lokairahaM kimuchye?
14 Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
tadAnIM te kathitavantaH, kechid vadanti tvaM majjayitA yohan, kechidvadanti, tvam eliyaH, kechichcha vadanti, tvaM yirimiyo vA kashchid bhaviShyadvAdIti|
15 Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
pashchAt sa tAn paprachCha, yUyaM mAM kaM vadatha? tataH shimon pitara uvAcha,
16 Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
tvamamareshvarasyAbhiShiktaputraH|
17 Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
tato yIshuH kathitavAn, he yUnasaH putra shimon tvaM dhanyaH; yataH kopi anujastvayyetajj nAnaM nodapAdayat, kintu mama svargasyaH pitodapAdayat|
18 Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs )
ato. ahaM tvAM vadAmi, tvaM pitaraH (prastaraH) aha ncha tasya prastarasyopari svamaNDalIM nirmmAsyAmi, tena nirayo balAt tAM parAjetuM na shakShyati| (Hadēs )
19 Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
ahaM tubhyaM svargIyarAjyasya ku njikAM dAsyAmi, tena yat ki nchana tvaM pR^ithivyAM bhaMtsyasi tatsvarge bhaMtsyate, yachcha ki nchana mahyAM mokShyasi tat svarge mokShyate|
20 Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
pashchAt sa shiShyAnAdishat, ahamabhiShikto yIshuriti kathAM kasmaichidapi yUyaM mA kathayata|
21 Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
anya ncha yirUshAlamnagaraM gatvA prAchInalokebhyaH pradhAnayAjakebhya upAdhyAyebhyashcha bahuduHkhabhogastai rhatatvaM tR^itIyadine punarutthAna ncha mamAvashyakam etAH kathA yIshustatkAlamArabhya shiShyAn j nApayitum ArabdhavAn|
22 Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
tadAnIM pitarastasya karaM ghR^itvA tarjayitvA kathayitumArabdhavAn, he prabho, tat tvatto dUraM yAtu, tvAM prati kadApi na ghaTiShyate|
23 Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
kintu sa vadanaM parAvartya pitaraM jagAda, he vighnakArin, matsammukhAd dUrIbhava, tvaM mAM bAdhase, IshvarIyakAryyAt mAnuShIyakAryyaM tubhyaM rochate|
24 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
anantaraM yIshuH svIyashiShyAn uktavAn yaH kashchit mama pashchAdgAmI bhavitum ichChati, sa svaM dAmyatu, tathA svakrushaM gR^ihlan matpashchAdAyAtu|
25 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
yato yaH prANAn rakShitumichChati, sa tAn hArayiShyati, kintu yo madarthaM nijaprANAn hArayati, sa tAn prApsyati|
26 Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
mAnuSho yadi sarvvaM jagat labhate nijapraNAn hArayati, tarhi tasya ko lAbhaH? manujo nijaprANAnAM vinimayena vA kiM dAtuM shaknoti?
27 Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
manujasutaH svadUtaiH sAkaM pituH prabhAveNAgamiShyati; tadA pratimanujaM svasvakarmmAnusArAt phalaM dAsyati|
28 “Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”
ahaM yuShmAn tathyaM vachmi, sarAjyaM manujasutam AgataM na pashyanto mR^ityuM na svAdiShyanti, etAdR^ishAH katipayajanA atrApi daNDAyamAnAH santi|