< Mattiyu 16 >

1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
tadAnIM phirUzinaH sidUkinazcAgatya taM parIkSituM nabhamIyaM kinjcana lakSma darzayituM tasmai nivEdayAmAsuH|
2 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
tataH sa uktavAn, sandhyAyAM nabhasO raktatvAd yUyaM vadatha, zvO nirmmalaM dinaM bhaviSyati;
3 da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
prAtaHkAlE ca nabhasO raktatvAt malinatvAnjca vadatha, jhanjbhzadya bhaviSyati| hE kapaTinO yadi yUyam antarIkSasya lakSma bOddhuM zaknutha, tarhi kAlasyaitasya lakSma kathaM bOddhuM na zaknutha?
4 Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
EtatkAlasya duSTO vyabhicArI ca vaMzO lakSma gavESayati, kintu yUnasO bhaviSyadvAdinO lakSma vinAnyat kimapi lakSma tAn na darzayiyyatE| tadAnIM sa tAn vihAya pratasthE|
5 Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
anantaramanyapAragamanakAlE tasya ziSyAH pUpamAnEtuM vismRtavantaH|
6 Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
yIzustAnavAdIt, yUyaM phirUzinAM sidUkinAnjca kiNvaM prati sAvadhAnAH satarkAzca bhavata|
7 Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
tEna tE parasparaM vivicya kathayitumArEbhirE, vayaM pUpAnAnEtuM vismRtavanta EtatkAraNAd iti kathayati|
8 Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
kintu yIzustadvijnjAya tAnavOcat, hE stOkavizvAsinO yUyaM pUpAnAnayanamadhi kutaH parasparamEtad viviMkya?
9 Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
yuSmAbhiH kimadyApi na jnjAyatE? panjcabhiH pUpaiH panjcasahasrapuruSESu bhOjitESu bhakSyOcchiSTapUrNAn kati PalakAn samagRhlItaM;
10 Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
tathA saptabhiH pUpaizcatuHsahasrapuruSESu bhEjitESu kati PalakAn samagRhlIta, tat kiM yuSmAbhirna smaryyatE?
11 Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
tasmAt phirUzinAM sidUkinAnjca kiNvaM prati sAvadhAnAstiSThata, kathAmimAm ahaM pUpAnadhi nAkathayaM, Etad yUyaM kutO na budhyadhvE?
12 Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
tadAnIM pUpakiNvaM prati sAvadhAnAstiSThatEti nOktvA phirUzinAM sidUkinAnjca upadEzaM prati sAvadhAnAstiSThatEti kathitavAn, iti tairabOdhi|
13 Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
aparanjca yIzuH kaisariyA-philipipradEzamAgatya ziSyAn apRcchat, yO'haM manujasutaH sO'haM kaH? lOkairahaM kimucyE?
14 Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
tadAnIM tE kathitavantaH, kEcid vadanti tvaM majjayitA yOhan, kEcidvadanti, tvam EliyaH, kEcicca vadanti, tvaM yirimiyO vA kazcid bhaviSyadvAdIti|
15 Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
pazcAt sa tAn papraccha, yUyaM mAM kaM vadatha? tataH zimOn pitara uvAca,
16 Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
tvamamarEzvarasyAbhiSiktaputraH|
17 Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
tatO yIzuH kathitavAn, hE yUnasaH putra zimOn tvaM dhanyaH; yataH kOpi anujastvayyEtajjnjAnaM nOdapAdayat, kintu mama svargasyaH pitOdapAdayat|
18 Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs g86)
atO'haM tvAM vadAmi, tvaM pitaraH (prastaraH) ahanjca tasya prastarasyOpari svamaNPalIM nirmmAsyAmi, tEna nirayO balAt tAM parAjEtuM na zakSyati| (Hadēs g86)
19 Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
ahaM tubhyaM svargIyarAjyasya kunjjikAM dAsyAmi, tEna yat kinjcana tvaM pRthivyAM bhaMtsyasi tatsvargE bhaMtsyatE, yacca kinjcana mahyAM mOkSyasi tat svargE mOkSyatE|
20 Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
pazcAt sa ziSyAnAdizat, ahamabhiSiktO yIzuriti kathAM kasmaicidapi yUyaM mA kathayata|
21 Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
anyanjca yirUzAlamnagaraM gatvA prAcInalOkEbhyaH pradhAnayAjakEbhya upAdhyAyEbhyazca bahuduHkhabhOgastai rhatatvaM tRtIyadinE punarutthAnanjca mamAvazyakam EtAH kathA yIzustatkAlamArabhya ziSyAn jnjApayitum ArabdhavAn|
22 Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
tadAnIM pitarastasya karaM ghRtvA tarjayitvA kathayitumArabdhavAn, hE prabhO, tat tvattO dUraM yAtu, tvAM prati kadApi na ghaTiSyatE|
23 Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
kintu sa vadanaM parAvartya pitaraM jagAda, hE vighnakArin, matsammukhAd dUrIbhava, tvaM mAM bAdhasE, IzvarIyakAryyAt mAnuSIyakAryyaM tubhyaM rOcatE|
24 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
anantaraM yIzuH svIyaziSyAn uktavAn yaH kazcit mama pazcAdgAmI bhavitum icchati, sa svaM dAmyatu, tathA svakruzaM gRhlan matpazcAdAyAtu|
25 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
yatO yaH prANAn rakSitumicchati, sa tAn hArayiSyati, kintu yO madarthaM nijaprANAn hArayati, sa tAn prApsyati|
26 Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
mAnuSO yadi sarvvaM jagat labhatE nijapraNAn hArayati, tarhi tasya kO lAbhaH? manujO nijaprANAnAM vinimayEna vA kiM dAtuM zaknOti?
27 Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
manujasutaH svadUtaiH sAkaM pituH prabhAvENAgamiSyati; tadA pratimanujaM svasvakarmmAnusArAt phalaM dAsyati|
28 “Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”
ahaM yuSmAn tathyaM vacmi, sarAjyaM manujasutam AgataM na pazyantO mRtyuM na svAdiSyanti, EtAdRzAH katipayajanA atrApi daNPAyamAnAH santi|

< Mattiyu 16 >