< Mattiyu 16 >
1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
And the Pharisees and Sadducees having come, tempting, did question him, to shew to them a sign from the heaven,
2 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
and he answering said to them, 'Evening having come, ye say, Fair weather, for the heaven is red,
3 da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
and at morning, Foul weather to-day, for the heaven is red — gloomy; hypocrites, the face of the heavens indeed ye do know to discern, but the signs of the times ye are not able!
4 Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
'A generation evil and adulterous doth seek a sign, and a sign shall not be given to it, except the sign of Jonah the prophet;' and having left them he went away.
5 Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
And his disciples having come to the other side, forgot to take loaves,
6 Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
and Jesus said to them, 'Beware, and take heed of the leaven of the Pharisees and Sadducees;'
7 Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
and they were reasoning in themselves, saying, 'Because we took no loaves.'
8 Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
And Jesus having known, said to them, 'Why reason ye in yourselves, ye of little faith, because ye took no loaves?
9 Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
do ye not yet understand, nor remember the five loaves of the five thousand, and how many hand-baskets ye took up?
10 Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
nor the seven loaves of the four thousand, and how many baskets ye took up?
11 Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
how do ye not understand that I did not speak to you of bread — to take heed of the leaven of the Pharisees and Sadducees?'
12 Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
Then they understood that he did not say to take heed of the leaven of the bread, but of the teaching, of the Pharisees and Sadducees.
13 Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
And Jesus, having come to the parts of Caesarea Philippi, was asking his disciples, saying, 'Who do men say me to be — the Son of Man?'
14 Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
and they said, 'Some, John the Baptist, and others, Elijah, and others, Jeremiah, or one of the prophets.'
15 Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
He saith to them, 'And ye — who do ye say me to be?'
16 Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
and Simon Peter answering said, 'Thou art the Christ, the Son of the living God.'
17 Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
And Jesus answering said to him, 'Happy art thou, Simon Bar-Jona, because flesh and blood did not reveal [it] to thee, but my Father who is in the heavens.
18 Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs )
'And I also say to thee, that thou art a rock, and upon this rock I will build my assembly, and gates of Hades shall not prevail against it; (Hadēs )
19 Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
and I will give to thee the keys of the reign of the heavens, and whatever thou mayest bind upon the earth shall be having been bound in the heavens, and whatever thou mayest loose upon the earth shall be having been loosed in the heavens.'
20 Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
Then did he charge his disciples that they may say to no one that he is Jesus the Christ.
21 Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
From that time began Jesus to shew to his disciples that it is necessary for him to go away to Jerusalem, and to suffer many things from the elders, and chief priests, and scribes, and to be put to death, and the third day to rise.
22 Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
And having taken him aside, Peter began to rebuke him, saying, 'Be kind to thyself, sir; this shall not be to thee;'
23 Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
and he having turned, said to Peter, 'Get thee behind me, adversary! thou art a stumbling-block to me, for thou dost not mind the things of God, but the things of men.'
24 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
Then said Jesus to his disciples, 'If any one doth will to come after me, let him disown himself, and take up his cross, and follow me,
25 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
for whoever may will to save his life, shall lose it, and whoever may lose his life for my sake shall find it,
26 Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
for what is a man profited if he may gain the whole world, but of his life suffer loss? or what shall a man give as an exchange for his life?
27 Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
'For, the Son of Man is about to come in the glory of his Father, with his messengers, and then he will reward each, according to his work.
28 “Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”
Verily I say to you, there are certain of those standing here who shall not taste of death till they may see the Son of Man coming in his reign.'