< Mattiyu 16 >

1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
And the Pharisees and Sadducees having come to Him, tempting Him, asked Him to show them a sign from heaven.
2 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
And He responding said to them, It being evening, you say, It will be fair weather: because the sky is red:
3 da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
and in the morning, It will be stormy to-day: for the lowering sky is red: ye hypocrites, you know how to discern the face of the sky: but are you not able to discern the signs of the times?
4 Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
A wicked and adulterous generation seeks after a sign. And no sign shall be given it, except the sign of the prophet Jonah. And leaving them, He departed.
5 Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
His disciples having come to the other side forgot to take bread.
6 Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
And Jesus said to them; See and beware of the leaven of the Pharisees and Sadducees.
7 Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
And they were reasoning among themselves, saying, That it is because we did not take bread.
8 Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
And Jesus knowing said to them, Why do you reason among yourselves, O ye of little faith, because you did not take bread?
9 Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
Do you not yet understand? do you not remember the five loaves of the five thousand, and how many baskets ye took up?
10 Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
Nor the seven loaves of the four thousand, and how many baskets you took up?
11 Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
How do you not understand that I did not speak to you concerning bread, to beware of the leaven of the Pharisees and the Sadducees.
12 Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
Then they understood that He did not say to beware of the leaven of the (bread) of the Pharisees and Sadducees, but of the teaching of the Pharisees and Sadducees.
13 Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
And Jesus having come into the regions of Caesarea Philippi, asked His disciples, saying, Whom do the people say that I, the Son of man, am?
14 Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
And they said, Some, John the Baptist; and some, Elijah; and others, Jeremiah, or one of the prophets.
15 Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
And He says to them, But whom do you say that I am?
16 Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
And Simon Peter responding said, Thou art the Christ, the Son of the living God.
17 Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
And Jesus responding said to him, Blessed art thou, Simon the son of Jonah: because flesh and blood did not reveal it to thee, but my Father who is in the heavens.
18 Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs g86)
And I say to thee, that thou art Peter, and upon this rock will I build my Church, and the gates of Hades shall not prevail against it. (Hadēs g86)
19 Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
And I will give unto thee the keys of the kingdom of the heavens: and whatsoever you may bind on the earth, shall be bound in the heavens; and whatsoever you may loose on earth shall be loosed in the heavens.
20 Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
Then He commanded His disciples that they should tell no one that He is the Christ.
21 Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
And from this time Jesus began to show to His disciples, that it behooves Him to go away to Jerusalem, and to suffer many things from the elders and the chief priest and the scribes, and to be killed, and rise the third day.
22 Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
And Peter taking Him to him, began to rebuke Him, saying, Be it far from thee, Lord; because this shall not be unto thee.
23 Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
And turning He said to Peter, Get behind me, adversary: thou art my stumbling-block; because thou art not thinking about the things of God, but those of men.
24 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
Then Jesus said to His disciples, If any one wishes to come after me, let him deny himself, and take up his cross, and follow me.
25 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
For whosoever may wish to save his soul shall lose it: and whosoever may lose his soul for my sake shall find it.
26 Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
For what is a man profited, if he may gain the whole world, and lose his own soul? or what will a man give in exchange for his soul?
27 Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
For the Son of man is about to come in the glory of His Father with His angels, and then He will give to each one according to his works.
28 “Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”
Truly I say unto you, There are some of those standing here, who may not taste of death, until they may see the Son of man coming in His kingdom.

< Mattiyu 16 >