< Mattiyu 16 >
1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
And the Pharisees and Sadducees came to tempt him, and asked him to show them a sign from heaven.
2 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
But he answered and said to them: When it is evening, you say, Fair weather; for the sky is red.
3 da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
And in the morning, A storm to-day; for the sky is red and lowering. Hypocrites! you know how to judge of the face of the sky; but you can not judge of the signs of the times.
4 Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
A wicked and adulterous generation seeks for a sign: and no sign shall be given it but the sign of Jonah the prophet. And he left them and departed.
5 Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
And his disciples came to the other side, and had forgotten to take bread.
6 Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
And Jesus said to them: Take heed and beware of the leaven of the Pharisees and Sadducees.
7 Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
And they reasoned among themselves, saying: It is because we took no bread.
8 Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
And Jesus perceiving it, said to them: O you of little faith! why are you reasoning among yourselves because you took no bread?
9 Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
Do you not yet understand, nor remember the five loaves of the five thousand, and how many baskets you took up?
10 Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
Nor the seven loaves of the four thousand, and how many baskets you took up?
11 Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
How is it that you do not understand, that I did not speak of bread when I commanded you to beware of the leaven of the Pharisees and of the Sadducees?
12 Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
Then they understood that he did not bid them beware of the leaven of bread, but of the teaching of the Pharisees and of the Sadducees.
13 Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
When Jesus came into the regions of Cæsarea Philippi, he asked his disciples, saying: Who do men say that I, the Son of man, am?
14 Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
They replied: Some say that thou art John the Immerser; others, Elijah; others, Jeremiah, or one of the prophets.
15 Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
He said to them: But who say you that I am?
16 Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
Simon Peter answered and said: Thou art the Christ, the Son of the living God.
17 Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
And Jesus answered and said to him: Blessed are you, Simon, son of Jonah; for flesh and blood did not reveal this to you, but my Father who is in heaven.
18 Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs )
And I say to you, That you are Peter, and on this rock I will build my church: and the gates of hades shall not prevail against it. (Hadēs )
19 Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
And I will give to you the keys of the kingdom of heaven; and whatever you shall bind on earth, shall be bound in heaven; and whatever you shall loose on earth, shall be loosed in heaven.
20 Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
Then he charged his disciples to tell no one that he was the Christ.
21 Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
From that time Jesus began to tell his disciples plainly, that he must go to Jerusalem, and suffer many things from the elders, and the chief priests, and the scribes, and be put to death, and be raised again the third day.
22 Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
And Peter took him and began to rebuke him, saying: Be it far from thee, Lord: this shall not be to thee.
23 Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
But he turned and said to Peter: Get behind me, adversary; you are a snare to me: for you are not thinking of the things of God; but of the things of men.
24 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
Then Jesus said to his disciples: If any one determines to come after me, let him deny himself, and take up his cross, and follow me.
25 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
For whoever will save his life, shall lose it. But whoever will lose his life for my sake, shall find it.
26 Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
For what is a man profited, if he gain the whole world, but lose his own life? Or, what will a man give as the ransom of his life?
27 Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
For the Son of man will come in the glory of his Father, with his angels; and then he will reward every one according to his deeds.
28 “Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”
Verily I say to you, There are some standing here that shall not taste of death, till they see the Son of man coming in his kingdom.