< Mattiyu 16 >
1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
Og Farisæerne og Saddukæerne kom hen og fristede ham og begærede, at han vilde vise dem et Tegn fra Himmelen.
2 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
Men han svarede og sagde til dem: „Om Aftenen sige I: Det bliver en skøn Dag, thi Himmelen er rød;
3 da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
og om Morgenen: Det bliver Storm i Dag, thi Himmelen er rød og mørk. Om Himmelens Udseende vide I at dømme, men om Tidernes Tegn kunne I det ikke.
4 Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
En ond og utro Slægt forlanger Tegn; men der skal intet Tegn gives den uden Jonas's Tegn.” Og han forlod dem og gik bort.
5 Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
Og da hans Disciple kom over til hin Side, havde de glemt at tage Brød med.
6 Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
Og Jesus sagde til dem: „Ser til, og tager eder i Vare for Farisæernes og Saddukæernes Surdejg!”
7 Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
Men de tænkte ved sig selv og sagde: „Det er, fordi vi ikke toge Brød med.”
8 Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
Men da Jesus mærkede dette, sagde han: „I lidettroende! hvorfor tænke I ved eder selv paa, at I ikke have taget Brød med?
9 Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
Forstaa I ikke endnu? Komme I heller ikke i Hu de fem Brød til de fem Tusinde, og hvor mange Kurve I da toge op?
10 Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
Ikke heller de syv Brød til de fire Tusinde, og hvor mange Kurve I da toge op?
11 Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
Hvorledes forstaa I da ikke, at det ej var om Brød, jeg sagde det til eder? Men tager eder i Vare for Farisæernes og Saddukæernes Surdejg.”
12 Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
Da forstode de, at han havde ikke sagt, at de skulde tage sig i Vare for Surdejgen i Brød, men for Farisæernes og Saddukæernes Lære.
13 Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
Men da Jesus var kommen til Egnen ved Kæsarea Filippi, spurgte han sine Disciple og sagde: „Hvem sige Folk, at Menneskesønnen er?”
14 Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
Men de sagde: „Nogle sige Johannes Døberen; andre Elias; andre Jeremias eller en af Profeterne.”
15 Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
Han siger til dem: „Men I, hvem sige I, at jeg er?”
16 Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
Da svarede Simon Peter og sagde: „Du er Kristus, den levende Guds Søn.”
17 Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
Og Jesus svarede og sagde til ham: „Salig er du, Simon Jonas's Søn! thi Kød og Blod har ikke aabenbaret dig det, men min Fader, som er i Himlene.
18 Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs )
Saa siger jeg ogsaa dig, at du er Petrus, og paa denne Klippe vil jeg bygge min Menighed, og Dødsrigets Porte skulle ikke faa Overhaand over den. (Hadēs )
19 Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
Og jeg vil give dig Himmeriges Riges Nøgler, og hvad du binder paa Jorden, det skal være bundet i Himlene, og hvad du løser paa Jorden, det skal være løst i Himlene.”
20 Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
Da bød han sine Disciple, at de maatte ikke sige til nogen, at han var Kristus.
21 Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
Fra den Tid begyndte Jesus at give sine Disciple til Kende, at han skulde gaa til Jerusalem og lide meget af de Ældste og Ypperstepræsterne og de skriftkloge og ihjelslaas og oprejses paa den tredje Dag.
22 Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
Og Peter tog ham til Side, begyndte at sætte ham i Rette og sagde: „Gud bevare dig, Herre; dette skal ingenlunde ske dig!”
23 Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
Men han vendte sig og sagde til Peter: „Vig bag mig, Satan! du er mig en Forargelse; thi du sanser ikke, hvad Guds er, men hvad Menneskers er.”
24 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
Da sagde Jesus til sine Disciple: „Vil nogen komme efter mig, han fornægte sig selv og tage sit Kors op og følge mig!
25 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
Thi den, som vil frelse sit Liv, skal miste det; men den, som mister sit Liv for min Skyld, skal bjærge det.
26 Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
Thi hvad gavner det et Menneske, om han vinder den hele Verden, men maa bøde med sin Sjæl? Eller hvad kan et Menneske give til Vederlag for sin Sjæl?
27 Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
Thi Menneskesønnen skal komme i sin Faders Herlighed med sine Engle; og da skal han betale enhver efter hans Gerning.
28 “Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”
Sandelig, siger jeg eder, der er nogle af dem, som staa her, der ingenlunde skulle smage Døden, førend de se Menneskesønnen komme i sit Rige.”