< Mattiyu 15 >
1 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
Тогда приступиша ко Иисусови иже от Иерусалима книжницы и фарисее, глаголюще:
2 “Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
почто ученицы Твои преступают предание старец? Не умывают бо рук своих, егда хлеб ядят.
3 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
Он же отвещав рече им: почто и вы преступаете заповедь Божию за предание ваше?
4 Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
Бог бо заповеда, глаголя: чти отца и матерь: и: иже злословит отца или матерь, смертию да умрет.
5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
Вы же глаголете: иже аще речет отцу или матери: дар, имже бы от мене пользовался еси:
6 ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
и да не почтит отца своего или матере: и разористе заповедь Божию за предание ваше.
7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
Лицемери, добре пророчествова о вас Исаиа, глаголя:
8 “‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
приближаются Мне людие сии усты своими и устнами чтут Мя: сердце же их далече отстоит от Мене:
9 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
всуе же чтут Мя, учаще учением, заповедем человеческим.
10 Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
И призвав народы, рече им: слышите и разумейте:
11 Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
не входящее во уста сквернит человека: но исходящее изо уст, то сквернит человека.
12 Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
Тогда приступльше ученицы Его реша Ему: веси ли, яко фарисее слышавше слово соблазнишася?
13 Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
Он же отвещав рече: всяк сад, егоже не насади Отец Мой Небесный, искоренится:
14 Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
оставите их: вожди суть слепи слепцем: слепец же слепца аще водит, оба в яму впадетася.
15 Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
Отвещав же Петр рече Ему: скажи нам притчу сию.
16 Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
Иисус же рече (им): единаче ли и вы без разума есте?
17 Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
Не у ли разумеваете, яко всяко, еже входит во уста, во чрево вмещается и афедроном исходит?
18 Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
Исходящая же изо уст, от сердца исходят, и та сквернят человека:
19 Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
от сердца бо исходят помышления злая, убийства, прелюбодеяния, любодеяния, татьбы, лжесвидетелства, хулы:
20 Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
сия суть сквернящая человека: а еже неумовенныма рукама ясти, не сквернит человека.
21 Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
И изшед оттуду Иисус, отиде во страны Тирския и Сидонския.
22 Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
И се, жена Хананейска, от предел тех изшедши, возопи к Нему глаголющи: помилуй мя, Господи, сыне Давидов, дщи моя зле беснуется.
23 Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
Он же не отвеща ей словесе. И приступльше ученицы Его, моляху Его, глаголюще: отпусти ю, яко вопиет вслед нас.
24 Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
Он же отвещав рече: несмь послан, токмо ко овцам погибшым дому Израилева.
25 Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
Она же пришедши поклонися Ему, глаголющи: Господи, помози ми.
26 Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
Он же отвещав рече: несть добро отяти хлеба чадом и поврещи псом.
27 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
Она же рече: ей, Господи: ибо и пси ядят от крупиц падающих от трапезы господей своих.
28 Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
Тогда отвещав Иисус рече ей: о, жено, велия вера твоя: буди тебе якоже хощеши. И изцеле дщи ея от того часа.
29 Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
И прешед оттуду Иисус, прииде на море Галилейское, и возшед на гору, седе ту.
30 Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
И приступиша к Нему народи мнози, имуще с собою хромыя, слепыя, немыя, бедныя и ины многи, и привергоша их к ногама Иисусовыма: и изцели их:
31 Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
якоже народом дивитися, видящым немыя глаголюща, бедныя здравы, хромыя ходящя и слепыя видящя: и славляху Бога Израилева.
32 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
Иисус же призвав ученики Своя, рече (им): милосердую о народе (сем), яко уже дни три приседят Мне и не имут чесо ясти: и отпустити их не ядших не хощу, да не како ослабеют на пути.
33 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
И глаголаша Ему ученицы Его: откуду нам в пустыни хлеби толицы, яко да насытится толик народ?
34 Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
И глагола им Иисус: колико хлебы имате? Они же реша: седмь, и мало рыбиц.
35 Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
И повеле народом возлещи на земли,
36 Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
и приемь седмь хлебы и рыбы, хвалу воздав преломи и даде учеником Своим, ученицы же народом.
37 Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
И ядоша вси и насытишася: и взяша избытки укрух, седмь кошниц исполнь:
38 Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
ядших же бяше четыре тысящы мужей, разве жен и детей.
39 Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.
И отпустив народы, влезе в корабль и прииде в пределы Магдалински.