< Mattiyu 15 >

1 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
Etu pichete Pharisee aru niyom likha manu khan Jerusalem pora Jisu usorte ahise. Taikhan koise,
2 “Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
“Kile Apuni laga chela khan bura khan banai diya niyom khan bhangai thake? Kile taikhan hath nadholai kene roti khai.”
3 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
Jisu taikhan ke jowab dikene koise, “Tinehoile kele tumikhan bhi nijor laga niyom nimite Isor laga niyom khan bhangai?
4 Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
Kilekoile Isor pora hukum dise, eneka koise, ‘Nijor laga baba aru ama ke sonman dibi,’ aru ‘Jun tai nijor baba aru ama laga biya kotha koi, tai hosa pora bhi moribo.’
5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
Kintu tumikhan koi, ‘Jun khan nijor baba nohoile bhi ama ke koi, “Ki modot apnikhan moi pora pabole ase eitu khan etiya pora Isor ke daan dibo,’”
6 ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
utu manu to tai laga baba ke sonman nadile bhi hobo. Eneka kori kene tumikhan Isor laga kotha ke hisab nathaka kori dise, tumikhan laga niyom manibo nimite.
7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
Dhungi khan! Isaiah pora thik koise, jitia tumikhan nimite tai bhabobani korise,
8 “‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
‘Etu manu khan Moike mukh pora he sonman kore, Kintu taikhan laga mon to Moi pora bisi dur te ase.
9 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
Taikhan Moike aradhana kora to misa-misi ase, Kile mane manu pora bana niyom khan taikhan nijor laga niyom nisena sikhai thake.’”
10 Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
Etu pichete Jisu pora joma hoi kene thaka manu khan ke mati kene koise, “Huni bhi aru bujhi bhi-
11 Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
Ki saman manu laga mukh te ghuse etu pora manu ke letera nakore. Kintu, ki to mukh pora bahar te ulai, etu pora he manu ke letera kori diye.”
12 Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
Etu pichete chela khan ahi kene Jisu ke koise, “Apuni jane na nai etu Pharisee khan jitia Apuni laga kotha hunise, taikhan khushi panai koi kene?”
13 Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
Jisu pora taikhan ke koise, “Sob ghas juntu sorgote thaka Ami laga Baba pora rupa nai, eitu khan sobke mati bhitor pora tani kene phelai dibo.”
14 Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
Taikhan ke ekla chari bhi, taikhan nijor andha koi kene andha manu ke rasta dikhai ase. Jitia ekta andha manu pora dusra andha manu ke rasta dikhai, tai duijon bhi nala te giri bo.”
15 Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
Peter jowab dikene Jisu ke koise, “Etu dristanto laga motlob to bujhai dibi.”
16 Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
Jisu koise, “Tumi etiya tak nabuji kene ase?
17 Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
Tumi najane, ki jinis mukh bhitor pora ghusi kene pet te jai, etu he pichete latrine kori kene bahar ulai koi kene?
18 Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
Kintu ji kotha khan mukh pora ulai eitu khan mon pora ulai. Eitu khan pora he manu ke letera kore.
19 Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
Kilekoile mon pora he biya bhabona, manu morai diya, bebichari, chor kora, misa gawahi, aru hinsa kora eitu khan ulai.
20 Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
Eitu khan pora he manu khan ke letera kore. Kintu hath nadholai kene kha pora manu ke letera nakore.”
21 Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
Etu pichete Jisu ta te pora ulai jaise, aru Tyre aru Sidon sheher phale jaise.
22 Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
Sabi, ta te ekjon Canaan laga mahila utu jaga pora ulaikene ahise. Tai hala kori kene koise, “Moi uporte daya koribi, Probhu, David laga Putro! Moi laga chukri gaw bhitor te bisi biya bhoot pora bandhi kene ase.”
23 Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
Kintu Jisu taike ekta jowab bhi diya nai. Tai laga chela khan ahi kene Taike anurodh koise, “Etu mahila ke khedai dibi, kele koile tai amikhan phale hala kori ase.”
24 Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
Kintu Jisu jowab dikene koise, “Kunba nimite moike patha nohoi, kintu Israel laga ghor laga harai ja mer khan nimite ase.”
25 Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
Kintu etu mahila ahise aru athukari kene Tai age te matha niche kori kene koise, “Probhu, amike modot koribi.”
26 Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
Tai jowab dikene koise, “Bacha khan laga roti loi kene kutta khan ke phelai kene diya to thik nohoi.”
27 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
Tai koise, “Hoi, Probhu, kintu kutta bacha khan bhi tai malik laga thali pora tukra gira khan khai.”
28 Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
Etu pichete Jisu etu mahila ke koise, “Maiki, tumi laga biswas to bisi dangor ase; tumi laga ki khushi ase thik eneka he hobo dibi.” Aru tai laga chukri utu somoite bhal hoi jaise.
29 Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
Jisu utu jaga ke chari kene Galilee Nodi usorte jaise. Etu pichete Tai pahar uporte jaise aru ta te bohise.
30 Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
Bisi manu joma koi kene Tai usorte ahise. Taikhan logote lengra, andha, juthor rugi bemar thaka, aru gunga khan, aru kisim bemar thaka manu khan ke loi kene ahise. Taikhan Jisu laga theng usorte anise aru Jisu pora taikhan ke bhal kori dise.
31 Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
Titia manu khan sob asurit hoise jitia taikhan kotha koribo napara khan kotha korise, lengera khan beraise, aru andha khan dikhi bole paise. Taikhan sob Israel laga Isor ke mohima dise.
32 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
Tai laga chela khan ke mati kene Jisu koise, “Etu manu khan nimite moi laga monte morom ase, kele koile taikhan tin din pora moi logote thakise aru taikhan ke khila bole eku bhi nai. Moi taikhan ke nakhilai kene pathai dibole mon nai, nohoile matha ghuri kene giri jabo pare.”
33 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
Tai laga chela khan Taike koise, “Etu nisena khali jagate kote pora amikhan iman bisi roti bisari kene manu khan ke khila bo?”
34 Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
Jisu taikhan ke koise, “Tumikhan logote kiman roti ase?” Taikhan koise, “Sat-ta, aru chutu maas khan olop ase.”
35 Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
Etu pichete Jisu manu khan ke matite bohibi koise.
36 Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
Tai sat-ta roti aru maas ke loise, aru dhanyavad diya pichete, roti bhangai kene chela khan ke dise. Aru chela khan pora manu khan ke bhag kori dise.
37 Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
Sob khaise aru pet bhorta hoise. Aru taikhan bacha roti sob joma korise aru sat-ta tukri bhorta hoise.
38 Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
Sob milaikena char hajar mota khan thakise, maiki aru bacha khan ke chari kene.
39 Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.
Etu pichete sobke nijor ghor te pathai dise aru Jisu ekta naw te uthi kene Magadan te jaise.

< Mattiyu 15 >