< Mattiyu 15 >

1 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
Alors des scribes et des pharisiens venus de Jérusalem s'approchèrent de Jésus, et lui dirent:
2 “Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
«Pourquoi tes disciples transgressent-ils la tradition des anciens? car ils ne se lavent pas les mains, quand ils prennent leur repas.
3 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
Il leur répondit: «Et vous, pourquoi transgressez-vous le commandement de Dieu par votre tradition?»
4 Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
Par exemple, Dieu a donné ce commandement: «Honore ton père et ta mère, » et: «Que celui qui maudit son père et sa mère, soit mis à mort; »
5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
mais vous, vous dites: «Celui qui dira à son père ou à sa mère: «Ce dont j'aurais pu vous assister, j'en ai fait offrande à Dieu; eh bien! qu'il n'honore pas son père et sa mère!»
6 ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
Ainsi vous mettez à néant le commandement de Dieu par votre tradition.
7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
Hypocrites, Ésaïe a bien prophétisé sur votre compte, quand il a dit:
8 “‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
«Ce peuple m'honore des lèvres mais son coeur est fort éloigné de moi.
9 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
C'est vainement qu'ils m'honorent, en donnant des préceptes qui ne sont que des commandements d'hommes.»
10 Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
Puis, ayant appelé la foule, il lui dit: «Écoutez et comprenez:
11 Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
Ce n'est pas ce qui entre dans la bouche qui souille l'homme; c'est ce qui sort de la bouche: voilà ce qui le ouille.»
12 Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
Alors les disciples s'approchèrent de lui, et lui dirent: «Sais-tu que les pharisiens ont été scandalisés de la parole qu'ils viennent d'entendre?»
13 Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
Jésus répondit: «Toute plante que mon Père céleste n'a pas plantée, sera arrachée.
14 Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
Laissez-les; ce sont des aveugles qui conduisent des aveugles. Si un aveugle en conduit un autre, ils tombent tous deux dans une fosse.»
15 Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
Pierre, prenant la parole, lui dit: «Explique-nous cette sentence.»
16 Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
— «Vous aussi, dit Jésus, vous êtes encore sans intelligence?
17 Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
Vous ne comprenez pas que tout ce qui entre dans la bouche, va dans le ventre et se rejette aux lieux;
18 Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
tandis que ce qui sort de la bouche, vient du coeur: voilà ce qui souille l'homme.
19 Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
Car c'est du coeur que sortent les mauvaises pensées, les meurtres, le libertinage, les vols, les faux témoignages, les calomnies.
20 Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
C'est là ce qui souille l'homme; mais de manger sans s'être lavé les mains, cela ne souille pas l'homme.»
21 Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
Jésus étant parti de là, se retira dans le territoire de Tyr et de Sidon.
22 Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
Et une Cananéenne qui venait de ces confins, lui dit à haute voix: «Seigneur, Fils de David, aie pitié de moi; ma fille est cruellement tourmentée par un démon.»
23 Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
Jésus ne lui répondit pas un mot. Ses disciples s'approchèrent de lui et le prièrent de la renvoyer: «Car, disaient-ils, elle nous poursuit de ses cris.»
24 Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
Jésus répondit: «Je n'ai été envoyé qu'aux brebis perdues de la maison d'Israël.»
25 Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
Mais cette femme vint se prosterner devant lui en disant: «Seigneur, secours-moi.»
26 Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
Il lui répondit: «Il n'est pas bien de prendre le pain des enfants pour le jeter aux petits chiens.»
27 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
Elle repartit: «Sans doute, Seigneur, puisque les petits chiens mangent les miettes qui tombent de la table de leurs maîtres.»
28 Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
Alors Jésus lui dit: «Femme, ta foi est grande; qu'il te soit fait comme tu le désires.» Dès cette heure sa fille fut guérie.
29 Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
Jésus, ayant quitté ces lieux, se rendit près de la mer de Galilée. Il monta sur la montagne, et s'assit.
30 Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
Une grande foule s'approcha de lui, ayant avec elle des boiteux, des aveugles, des sourds-muets, des estropiés et beaucoup d'autres malades. Elle les mit aux pieds de Jésus, et il les guérit,
31 Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
de sorte que la foule était dans l'admiration en voyant des muets parler, des estropiés être guéris, des boiteux marcher, des aveugles voir; et elle glorifia le Dieu d'Israël.
32 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
Jésus, avant appelé ses disciples, leur dit: «J'ai compassion de cette foule, car voilà déjà trois jours que ces gens restent près de moi, et ils n'ont pas de quoi manger. Je ne veux pas les renvoyer à jeun, de peur qu'ils ne défaillent en route.
33 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
Sur quoi ses disciples lui dirent: «où trouver en un désert assez de pains, pour nourrir tant de monde.»
34 Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
Et Jésus leur dit: «Combien avez-vous de pains?» — «Sept, dirent-ils, et quelques petits poissons.»
35 Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
Alors il fit asseoir la foule par terre,
36 Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
puis il prit les sept pains et les poissons, et, ayant rendu grâces, il les rompit et les donna à ses disciples, et les disciples les donnèrent à la foule.
37 Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
Tous mangèrent et furent rassasiés, et l'on emporta sept corbeilles pleines des morceaux qui restaient.
38 Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
Le nombre de ceux qui mangèrent s'élevait à quatre mille hommes, sans compter les femmes et les enfants.
39 Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.
Après avoir renvoyé la foule, Jésus entra dans la barque et gagna le territoire de Magadan.

< Mattiyu 15 >