< Mattiyu 15 >

1 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
Then came to Jesus the scribes and pharisees from Jerusalem saying,
2 “Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
Why do thy disciples transgress the tradition of the elders? for they wash not their hands when they eat.
3 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
But He answered and said unto them, And why do ye transgress the commandment of God for your tradition?
4 Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
For God commanded saying, Honour thy father and thy mother; and, He that revileth father or mother, let him be put to death:
5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
but ye say, If any man say to his father or mother, "that which thou mightest be profited by from me is a gift to the temple,"
6 ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
and so honour not his father or his mother, he shall be free. And thus have ye made void the commandment of God by your tradition.
7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
Well did Esaias prophecy concerning you,
8 “‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
saying, This people approach me with their mouth, and honour me with their lips, but their heart is far from me:
9 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
but in vain do they worship me, teaching for doctrines the injunctions of men.
10 Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
And He called the multitude to Him, and said unto them, Hear and understand it:
11 Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
not that which goeth into the mouth defileth the man; but that which cometh out of the mouth, this polluteth the man.
12 Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
Whereupon his disciples came and said to Him, Dost thou know that the pharisees, when they heard this assertion, were offended at it?
13 Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
But He answered and said, Every plantation which my heavenly Father hath not planted shall be rooted up.
14 Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
Regard them not; for they are blind guides of the blind: and if the blind lead the blind, both will fall into the ditch.
15 Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
Then Peter answered, and said unto Him, Explain to us this parable.
16 Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
And Jesus replied, Are ye also still void of understanding?
17 Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
Do ye not yet know, that whatever goeth into the mouth passeth to the belly and is discharged downwards?
18 Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
But the things, which proceed out of the mouth, come from the heart, and those defile a man.
19 Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
For out of the heart proceed wicked disputings, murders, adulteries, fornications, thefts, false-witnessings, slanders:
20 Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
these defile a man, but to eat without washing the hands doth not defile him.
21 Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
And Jesus went from thence, and retired into the parts adjacent to Tyre and Sidon.
22 Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
And there came out of those quarters a Canaanitish woman, and cried to Him saying, Have mercy on me, O Lord, thou son of David; for my daughter is grievously tormented by a demon.
23 Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
But he answered her not a word: and his disciples came and intreated Him, saying, Send her away, for she crieth importunately after us.
24 Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
But he answered and said, I am sent only to the lost sheep of the house of Israel.
25 Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
However, she came and worshipped Him, saying, Lord help me.
26 Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
But he answered, It is not fit to take the children's bread and throw it to dogs: and she said, True, Lord;
27 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
yet the dogs eat of the crumbs that fall from the table of their masters.
28 Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
Then Jesus answering, said unto her, O woman, great is thy faith: be it therefore unto thee as thou desirest. And her daughter was cured from that very hour.
29 Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
And Jesus departed from thence, and came near to the sea of Galilee; and going up to a mountain He sat down there.
30 Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
And great multitudes came to Him, having with them those that were lame, blind, dumb, maimed, and many others; and laid them at the feet of Jesus, and He healed them.
31 Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
So that the people wondered when they saw the dumb speaking, the maimed become sound, the lame walking, and the blind seeing: and they glorified the God of Israel.
32 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
Then Jesus called his disciples to Him and said, I am moved with compassion to the multitude, for they have been with me now three days, and have nothing to eat: I will not let them go away fasting, least they faint in the way.
33 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
And his disciples replied, Whence can we have so much bread in this desert place as to satisfy so great a multitude?
34 Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
And Jesus saith unto them, How many loaves have ye? and they said, Seven, and a few small fishes.
35 Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
Then He bid the people sit down on the ground;
36 Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
and taking the seven loaves and the fishes, when He had given thanks, He brake them, and gave to his disciples, and the disciples to the multitude.
37 Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
And they did all eat, and were satisfied: and they took up what was left even of fragments seven baskets full.
38 Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
Now they that did eat were four thousand men, beside women and children.
39 Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.
Then he dismissed the multitudes, and went into a ship, and came to the coasts of Magdala.

< Mattiyu 15 >