< Mattiyu 15 >

1 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
Then there came to Jesus a party of Pharisees and Scribes from Jerusalem, who inquired,
2 “Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
"Why do your disciples transgress the tradition of the Elders by not washing their hands before meals?"
3 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
"Why do you, too," He retorted, "transgress God's commands for the sake of your tradition?
4 Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
For God said, 'Honour thy father and thy mother'; and 'Let him who reviles father or mother be certainly put to death';
5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
but you--this is what you say: 'If a man says to his father or mother, That is consecrated, whatever it is, which otherwise you should have received from me--
6 ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
he shall be absolved from honouring his father'; and so you have abrogated God's Word for the sake of your tradition.
7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
Hypocrites! well did Isaiah prophesy of you,
8 “‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
"'This is a People who honour Me with their lips, while their heart is far away from Me;
9 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
but it is in vain they worship Me, while they lay down precepts which are mere human rules.'"
10 Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
Then, when He had called the people to Him, Jesus said, "Hear and understand.
11 Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
It is not what goes into a man's mouth that defiles him; but it is what comes out of his mouth--that defiles a man."
12 Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
Then His disciples came and said to Him, "Do you know that the Pharisees were greatly shocked when they heard those words?"
13 Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
"Every plant," He replied, "which my Heavenly Father has not planted will be rooted up.
14 Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
Leave them alone. They are blind guides of the blind; and if a blind man leads a blind man, both will fall into some pit."
15 Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
"Explain to us this figurative language," said Peter.
16 Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
"Are even you," He answered, "still without intellingence?
17 Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
Do you not understand that whatever enters the mouth passes into the stomach and is afterwards ejected from the body?
18 Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
But the things that come out of the mouth proceed from the heart, and it is these that defile the man.
19 Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
For out of the heart proceed wicked thoughts, murder, adultery, fornication, theft, perjury, impiety of speech.
20 Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
These are the things which defile the man; but eating with unwashed hands does not defile."
21 Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
Leaving that place, Jesus withdrew into the vicinity of Tyre and Sidon.
22 Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
Here a Canaanitish woman of the district came out and persistently cried out, "Sir, Son of David, pity me; my daughter is cruelly harassed by a demon."
23 Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
But He answered her not a word. Then the disciples interposed, and begged Him, saying, "Send her away because she keeps crying behind us."
24 Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
"I have only been sent to the lost sheep of the house of Israel," He replied.
25 Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
Then she came and threw herself at His feet and entreated Him. "O Sir, help me," she said.
26 Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
"It is not right," He said, "to take the children's bread and throw it to the dogs."
27 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
"Be it so, Sir," she said, "for even the dogs eat the scraps which fall from their masters' tables."
28 Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
"O woman," replied Jesus, "great is your faith: be it done to you as you desire." And from that moment her daughter was restored to health.
29 Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
Again, moving thence, Jesus went along by the Lake of Galilee; and ascending the hill, He sat down there.
30 Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
Soon great crowds came to Him, bringing with them those who were crippled in feet or hands, blind or dumb, and many besides, and they hastened to lay them at His feet. And He cured them,
31 Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
so that the people were amazed to see the dumb speaking, the maimed with their hands perfect, the lame walking, and the blind seeing; and they gave the glory to the God of Israel.
32 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
But Jesus called His disciples to Him and said, "My heart yearns over this mass of people, for it is now the third day that they have been with me and they have nothing to eat. I am unwilling to send them away hungry, lest they should faint on the road."
33 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
"Where can we," asked the disciples, "get bread enough in this remote place to satisfy so vast a multitude?"
34 Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
"How many loaves have you?" Jesus asked. "Seven," they said, "and a few small fish."
35 Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
So He bade all the people sit down on the ground,
36 Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
and He took the seven loaves and the fish, and after giving thanks He broke them up and then distributed them to the disciples, and they to the people.
37 Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
And they all ate and were satisfied. The broken portions that remained over they took up--seven full hampers.
38 Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
Those who ate were 4,000 adult men, without reckoning women and children.
39 Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.
He then dismissed the people, went on board the boat, and came into the district of Magadan.

< Mattiyu 15 >