< Mattiyu 15 >
1 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
Then the scribes and the Pharisees came to him from Jerusalem, saying:
2 “Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
“Why do your disciples transgress the tradition of the elders? For they do not wash their hands when they eat bread.”
3 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
But responding, he said to them: “And why do you transgress the commandment of God for the sake of your tradition? For God said:
4 Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
‘Honor your father and mother,’ and, ‘Whoever will have cursed father or mother shall die a death.’
5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
But you say: ‘If anyone will have said to father or mother, “It is dedicated, so that whatever is from me will benefit you,”
6 ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
then he shall not honor his father or his mother.’ So have you nullified the commandment of God, for the sake of your tradition.
7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
Hypocrites! How well did Isaiah prophesy about you, saying:
8 “‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
‘This people honors me with their lips, but their heart is far from me.
9 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
For in vain do they worship me, teaching the doctrines and commandments of men.’”
10 Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
And having called the multitudes to him, he said to them: “Listen and understand.
11 Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
A man is not defiled by what enters into the mouth, but by what proceeds from the mouth. This is what defiles a man.”
12 Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
Then his disciples drew near and said to him, “Do you know that the Pharisees, upon hearing this word, were offended?”
13 Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
But in response he said: “Every plant which has not been planted by my heavenly Father shall be uprooted.
14 Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
Leave them alone. They are blind, and they lead the blind. But if the blind are in charge of the blind, both will fall into the pit.”
15 Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
And responding, Peter said to him, “Explain this parable to us.”
16 Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
But he said: “Are you, even now, without understanding?
17 Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
Do you not understand that everything that enters into the mouth goes into the gut, and is cast into the sewer?
18 Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
But what proceeds from the mouth, goes forth from the heart, and those are the things that defile a man.
19 Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
For from the heart go out evil thoughts, murders, adulteries, fornications, thefts, false testimonies, blasphemies.
20 Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
These are the things that defile a man. But to eat without washing hands does not defile a man.”
21 Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
And departing from there, Jesus withdrew into the areas of Tyre and Sidon.
22 Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
And behold, a woman of Canaan, going out from those parts, cried out, saying to him: “Take pity on me, Lord, Son of David. My daughter is badly afflicted by a demon.”
23 Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
He did not say a word to her. And his disciples, drawing near, petitioned him, saying: “Dismiss her, for she is crying out after us.”
24 Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
And responding, he said, “I was not sent except to the sheep who have fallen away from the house of Israel.”
25 Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
But she approached and adored him, saying, “Lord, help me.”
26 Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
And responding, he said, “It is not good to take the bread of the children and cast it to the dogs.”
27 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
But she said, “Yes, Lord, but the young dogs also eat from the crumbs that fall from the table of their masters.”
28 Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
Then Jesus, responding, said to her: “O woman, great is your faith. Let it be done for you just as you wish.” And her daughter was healed from that very hour.
29 Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
And when Jesus had passed from there, he arrived beside the sea of Galilee. And ascending onto a mountain, he sat down there.
30 Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
And great multitudes came to him, having with them the mute, the blind, the lame, the disabled, and many others. And they cast them down at his feet, and he cured them,
31 Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
so much so that the crowds wondered, seeing the mute speaking, the lame walking, the blind seeing. And they magnified the God of Israel.
32 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
And Jesus, calling together his disciples, said: “I have compassion on the crowds, because they have persevered with me now for three days, and they do not have anything to eat. And I am not willing to dismiss them, fasting, lest they faint along the way.”
33 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
And the disciples said to him: “From where, then, in the desert, would we obtain enough bread to satisfy so a great multitude?”
34 Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
And Jesus said to them, “How many loaves of bread do you have?” But they said, “Seven, and a few little fish.”
35 Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
And he instructed the crowds to recline upon the ground.
36 Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
And taking the seven loaves and the fish, and giving thanks, he broke and gave to his disciples, and the disciples gave to the people.
37 Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
And they all ate and were satisfied. And, from what was left over of the fragments, they took up seven full baskets.
38 Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
But those who ate were four thousand men, plus children and women.
39 Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.
And having dismissed the crowd, he climbed into a boat. And he went into the coastal region of Magadan.