< Mattiyu 15 >
1 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
Then some Pharisees and scribes came to Jesus from Jerusalem and asked,
2 “Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
“Why do Your disciples break the tradition of the elders? They do not wash their hands before they eat.”
3 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
Jesus replied, “And why do you break the command of God for the sake of your tradition?
4 Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
For God said, ‘Honor your father and mother’ and ‘Anyone who curses his father or mother must be put to death.’
5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
But you say that if anyone says to his father or mother, ‘Whatever you would have received from me is a gift devoted to God,’
6 ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
he need not honor his father or mother with it. Thus you nullify the word of God for the sake of your tradition.
7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
You hypocrites! Isaiah prophesied correctly about you:
8 “‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
‘These people honor Me with their lips, but their hearts are far from Me.
9 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
They worship Me in vain; they teach as doctrine the precepts of men.’”
10 Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
Jesus called the crowd to Him and said, “Listen and understand.
11 Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
A man is not defiled by what enters his mouth, but by what comes out of it.”
12 Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
Then the disciples came to Him and said, “Are You aware that the Pharisees were offended when they heard this?”
13 Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
But Jesus replied, “Every plant that My heavenly Father has not planted will be pulled up by its roots.
14 Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
Disregard them! They are blind guides. If a blind man leads a blind man, both will fall into a pit.”
15 Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
Peter said to Him, “Explain this parable to us.”
16 Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
“Do you still not understand?” Jesus asked.
17 Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
“Do you not yet realize that whatever enters the mouth goes into the stomach and then is eliminated?
18 Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
But the things that come out of the mouth come from the heart, and these things defile a man.
19 Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
For out of the heart come evil thoughts, murder, adultery, sexual immorality, theft, false testimony, and slander.
20 Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
These are what defile a man, but eating with unwashed hands does not defile him.”
21 Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
Leaving that place, Jesus withdrew to the district of Tyre and Sidon.
22 Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
And a Canaanite woman from that region came to Him, crying out, “Lord, Son of David, have mercy on me! My daughter is miserably possessed by a demon.”
23 Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
But Jesus did not answer a word. So His disciples came and urged Him, “Send her away, for she keeps crying out after us.”
24 Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
He answered, “I was sent only to the lost sheep of the house of Israel.”
25 Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
The woman came and knelt before Him. “Lord, help me!” she said.
26 Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
But Jesus replied, “It is not right to take the children’s bread and toss it to the dogs.”
27 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
“Yes, Lord,” she said, “even the dogs eat the crumbs that fall from their master’s table.”
28 Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
“O woman,” Jesus answered, “your faith is great! Let it be done for you as you desire.” And her daughter was healed from that very hour.
29 Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
Moving on from there, Jesus went along the Sea of Galilee. Then He went up on a mountain and sat down.
30 Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
Large crowds came to Him, bringing the lame, the blind, the crippled, the mute, and many others, and laid them at His feet, and He healed them.
31 Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
The crowd was amazed when they saw the mute speaking, the crippled restored, the lame walking, and the blind seeing. And they glorified the God of Israel.
32 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
Then Jesus called His disciples to Him and said, “I have compassion for this crowd, because they have already been with Me three days and have nothing to eat. I do not want to send them away hungry, or they may faint along the way.”
33 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
The disciples replied, “Where in this desolate place could we find enough bread to feed such a large crowd?”
34 Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
“How many loaves do you have?” Jesus asked. “Seven,” they replied, “and a few small fish.”
35 Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
And He instructed the crowd to sit down on the ground.
36 Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
Taking the seven loaves and the fish, He gave thanks and broke them. Then He gave them to the disciples, and the disciples gave them to the people.
37 Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
They all ate and were satisfied, and the disciples picked up seven basketfuls of broken pieces that were left over.
38 Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
A total of four thousand men were fed, in addition to women and children.
39 Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.
After Jesus had dismissed the crowds, He got into the boat and went to the region of Magadan.