< Mattiyu 14 >

1 A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
Unsiki ghula untwa UHelode alyapuliike imhola sa Yesu.
2 sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
Pe akavavuula avavombi vaake akati, “Ujuo ghwe Yohani uMwofughi, asyukile kuhuma ku vafue, fye nambe ali ni ngufu isa kuvomba ifidegho.”
3 To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
UHelode alyajovile enendiiki ulwakuva alyankolile uYohani, akankunga na kukun'dindila mu ndinde. UYohani alyadindilue mu vwimila uHelodia un'dala ghwa Filipo, unnuuna ghwa Helode.
4 gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
Alyadindilue mu ndinde ulwakuva alyam'bulile luno nalunoghiile mu ndaghilo sa Nguluve.”
5 Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
UHelode ujuo akalondagha kukum'buda uYohani neke akoghopagha avaanhu ulwakuva valyankagwile uYohani kuuti m'bili.
6 A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
Lino, pa kikulukulu ikya kukumbuka kuholua untwa uHelode, umwalive ghwa Helodia akaseeja pamaso gha vahesia. Umhinja ujuo akamhovosia fiijo UHelode,
7 har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
Kuhanga akajiigha kukumpela kino ilonda kusuuma.
8 Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
Neke umhinja jula akahongua nu ng'ina ikya kusuuma, akam'buula uHelode akati, “Nilonda umheele lino lino umutu ghwa Yohani uMwafughi mu lisinia.”
9 Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
Untwa uHelode akasukunala kyongo. Neke ulwakuva akajighile pamaaso gha vahesia vala, akalaghila kuuti umhinja jula apelue.
10 ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
Pe akasuung'ha umuunhu alute mu ndinde adumule umutu ghwa Yohani.
11 Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
Umutu ghwa Yohani ghukaletua mu lisinia, akapelua umhunja jula, ghwope akampeela ung'ina.
12 Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
Pepano avavulanisivua va Yohani vakaluta, vakatoola um'bili ghwa Yohani, vakaghuviika mu mbiipa. Pe vakaluta kukum'buula uYesu imhola jila.
13 Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
UYesu ye apuliike imhola ijio, akavuuka pala ni ngalava na kuluta pamonga pa vusyefu. Neke avaanhu ye vapuliike kuuti uYesu avukile pala, vakahuma mu makaaja ghaave, vakaghenda lughulu, vikum'bingilila uYesu kuno alutile.
14 Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
UYesu ye ikwika mu ngalava, akalivona ilipugha ilivaha ilya vaanhu, akavavonela ikisa, akavasosia avatamu vaave.
15 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
Ye vwilile, avavulanisivua vaake vakaluta pa mwene vakam'buula vakati, “apa tukalile pe lunyika pasila kimonga, kange vwimile uvatavule avaanhu ava valutaghe mu fikaaja kuuti vakaghule ifyakulia.”
16 Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
UYesu akavamula akati, “Nakwekuti umpaka aveene avavuuke, muvapeele umue ikyakulia.”
17 Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
Aveene vakamula vakati, “Natuli ni kimonga apa, looli ghali gha makate ghahaano ni samaki ivili.”
18 Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
UYesu akavavuula akati, “Muleete apa”
19 Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
Pepano akavavuula avaanhu kuuti vikale pa lisoli. Pe akatoola amakate ghala ghahaano ni samaki sila ivili, akalolla kukyanya, akamhongesia uNguluve. Pe akamenyulania amakate ghala, akavapeela avavulanisivua vaake, voope vakavaghavilaavaanhu.
20 Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
Avaanhu vakalia, vakikuta. Avavulanisivua vaake vakakong'hania ifisighasi, sikamema indiilo kijigho ni vili.
21 Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
Avaanhu vano valyaliile, avakinhaata veene valyale imbilima ihaano, kisila kuvala avakijuuva na vaana.
22 Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
Unsiki ghughuo, UYesu akavavuula avavulanisivua vaake kuuti vingile mu ngalava, valongole kuluta imwambo ijingi, pano umwene itavula ilipugha lya vaanhu kuuti valutaghe.
23 Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
Ye avatavwile, akaluta mwene ku kilunda kukufunya. Ing'hiisi jikatengula, ajiighe mwene ku kidunda.
24 jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
Unsiki ughuo ingalava jila jikava jifikile pakate pa lisumbe, jitovua na mavingo, ulwakuva imhepo imbaha jikasighagha kuno viluta.
25 Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
Ye kutapihenga, uYesu akaluta ku vavulanisivua vaake, ighenda pakyanya pa malenga.
26 Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
Neke avavulanisivua vaake ye vikumwagha ighenda pakyanya pa malenga, vakoghopa kyongo, vakakoola vakati, “Ilisyuka”.
27 Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
Unsiki ghughuo uYesu akavavuula akati, “Kangala, neene, namungoghopaghe”
28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
Pe uPeteli akam'buula akati, “Ghwe Mutwa, nave lweli veeve, umbuule niise palyuve nighende pakyanya pa malenga.”
29 Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
UYesu akamwamula akati, “Isa” pe uPeteli akiikka mu ngalava jila, akatengula pighenda pakyanya pa malenga, iluta kwa Yesu.
30 Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
Neke ye ivona imhepo imbaha jigugula, akaghopa kyongo, akatengulakundwiila. Pe akakoola akati, “Ghwe Mutwa, umhooke!'
31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
Nakalingi, UYesu akagholosia uluvoko lwake, akankola, akam'buula akati, “Ghwe nya lwitiko ludebe uve, kiki uli ni nganighani?
32 Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
Pepano uYesu nu uPeteli vakingila mu ngalava, imhepo jila jikalitima.
33 Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
avavulanisivua vano valyale mu ngalava, vakamwimika uYesu vakati, “kyang'haani, uve uli Mwana ghwa Nguluve!'
34 Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
UYesu na vavulanisivua vaake vakalovoka ilisumbe ilya Galilaya, vakafika mu iisi ija Genesaleti.
35 Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
Avaanhu ava pala ye vakagwila kuuti ghwe Yesu, vakatwala imhola imbale sooni. Pepano avaanhu vakavatwala avatamu vooni kwa Yesu,
36 suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.
Vakansuuma avitikisie avatamu vabasie lu luvilo lwa mwenda ghwake. Avatamu vooni vano vakabasyagha, vakasokagha.

< Mattiyu 14 >