< Mattiyu 14 >

1 A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
V tem času zasliši četrtnik Herod glas o Jezusu,
2 sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
Ter reče hlapcem svojim: Ta je Janez Krstnik; on je vstal od mrtvih, in za to dela čudeže.
3 To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
Kajti Herod je bil Janeza vjel in ga vklenil in posadil v ječo, za voljo Herodijade, svojega brata Filipa žene.
4 gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
Kajti Janez mu je djal: Ni ti dovoljeno nje imeti.
5 Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
In hotel ga je umoriti; ali zbal se je ljudstva, ker so ga imeli za preroka.
6 A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
Ko je bil pa Herodovega rojstva dan, plesala je po sredi Herodijadina hči, in ugodila je Herodu.
7 har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
Za to jej s prisego obreče dati, karkoli bi prosila.
8 Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
Ona pa, naučena od matere svoje: Daj mi, reče, tu v skledi glavo Janeza Krstnika.
9 Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
In kralju se užali. Pa za voljo prisege in gostov jej ukaže dati.
10 ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
In pošlje, in odseka Janezu v ječi glavo.
11 Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
Ter prinesó glavo njegovo v skledi, in dadó jo dekletu; in nese jo materi svojej.
12 Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
In prišedši učenci njegovi, vzemó truplo in ga pokopljejo; ter pridejo in sporočé Jezusu.
13 Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
In slišavši to Jezus, odrine odtod na ladji posebej na samoten kraj. In ko ljudstvo to sliši, odidejo peš za njim iz mest.
14 Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
In Jezus izide in ugleda mnogo ljudstva; in zasmilijo mu se, ter uzdravi njih bolnike.
15 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
Ko se je pa zvečerilo, pristopijo k njemu učenci njegovi, govoreč: Kraj je samoten, in ura uže pozna; razpusti ljudstvo, da odidejo v vasí in si kupijo živeža.
16 Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
Jezus jim pa reče: Ni jim treba oditi; dajte jim vi jesti.
17 Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
Oni mu pa rekó: Nimamo več tu nego pet hlebov in dve ribi,
18 Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
On pa reče: Prinesite jih sem!
19 Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
Ter ukaže ljudstvu, naj sedejo po travi, in vzeme petere hlebe in tisti dve ribi, in pogledavši na nebo, blagoslovi; ter prelomi in dá hlebe učencem, učenci pa ljudstvu.
20 Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
In jedli so vsi, in nasitili so se; in pobrali so ostanke koscev, dvanajst košev polnih.
21 Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
Bilo jih je pa, kteri so jedli, kakih pet tisoči móž, brez žen in otrók.
22 Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
In precej prisili Jezus učence svoje, naj stopijo v ladjo, in gredó naprej na drugo stran, dokler ne razpustí ljudstva.
23 Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
In razpustivši ljudstvo, odide sam posebej na goro molit. Ko se je pa zvečerilo, bil je sam tu.
24 jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
Ladja je bila pa uže sredi morja, in valovi so jo metali; kajti bil je veter nasproti.
25 Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
O četrtej straži po noči pa odide Jezus k njim, hodé po morji.
26 Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
In ko ga učenci ugledajo, da hodi po morji, ustrašijo se in rekó: Prikazen je! in od strahu zakričé.
27 Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
Jezus jih pa precej ogovorí, in reče: Bodite srčni! Jaz sem; ne bojte se.
28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
Peter mu pa odgovorí in reče: Gospod! če si ti, ukaži mi, naj pridem k tebi pò vodi.
29 Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
On pa reče: Pridi! In stopivši Peter iz ladje, hodil je po vodi, da pride k Jezusu.
30 Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
Ko pa vidi, da je veter močán, uplaši se; in ko se začne potapljati, zavpije, govoreč; Gospod, otmi me!
31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
Jezus pa precej stegne roko in ga prime, ter mu reče: Maloverni! po kaj si dvomil?
32 Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
In ko stopita v ladjo, veter utihne.
33 Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
Tisti pa, ki so bili v ladji, pristopijo, ter mu se poklonijo, govoreč: Resnično si sin Božji!
34 Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
In prepeljavši se, pridejo v zemljo Genezaretsko.
35 Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
In ko ga tega kraja možjé spoznajo, pošljejo po vsej tistej okolici; in prinesó mu vse bolnike.
36 suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.
In prosili so ga, da bi se le robú obleke njegove dotaknili. In kterikoli so se dotaknili, ozdraveli so.

< Mattiyu 14 >