< Mattiyu 14 >
1 A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
En ce temps-là Hérode le tétrarque entendit ce qu'on publiait de Jésus;
2 sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
Et il dit à ses serviteurs: C'est Jean-Baptiste; il est ressuscité des morts, et c'est pour cela qu'il se fait des miracles par lui.
3 To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
Car Hérode avait fait prendre Jean, et l'avait fait lier et mettre en prison, au sujet d'Hérodias, femme de Philippe, son frère;
4 gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
Parce que Jean lui avait dit: Il ne t'est pas permis de l'avoir pour femme.
5 Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
Et il aurait bien voulu le faire mourir; mais il craignait le peuple, parce qu'on regardait Jean comme un prophète.
6 A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
Or, comme on célébrait le jour de la naissance d'Hérode, la fille d'Hérodias dansa au milieu de l'assemblée, et plut à Hérode;
7 har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
De sorte qu'il lui promit avec serment de lui donner tout ce qu'elle demanderait.
8 Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
Poussée par sa mère, elle lui dit: Donne-moi ici, dans un plat, la tête de Jean-Baptiste.
9 Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
Et le roi en fut fâché; mais à cause de son serment et de ceux qui étaient à table avec lui, il commanda qu'on la lui donnât.
10 ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
Et il envoya couper la tête à Jean dans la prison.
11 Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
Et on apporta sa tête dans un plat, et on la donna à la fille, et elle la présenta à sa mère.
12 Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
Puis ses disciples vinrent, et emportèrent son corps, et l'ensevelirent; et ils vinrent l'annoncer à Jésus.
13 Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
Et Jésus, l'ayant appris, se retira de là dans une barque, en un lieu écarté, à part. Et quand le peuple le sut, il sortit des villes et le suivit à pied.
14 Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
Et Jésus, étant sorti, vit une grande multitude; et il fut ému de compassion envers eux, et guérit leurs malades.
15 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
Et comme il se faisait tard, ses disciples vinrent à lui, et dirent: Ce lieu est désert, et l'heure est déjà avancée; renvoie ce peuple afin qu'ils aillent dans les bourgades, et qu'ils y achètent des vivres.
16 Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
Mais Jésus leur dit: Il n'est pas nécessaire qu'ils y aillent; donnez-leur vous-mêmes à manger.
17 Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
Et ils lui dirent: Nous n'avons ici que cinq pains et deux poissons.
18 Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
Et il dit: Apportez-les-moi ici.
19 Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
Et après avoir commandé que le peuple s'assît sur l'herbe, il prit les cinq pains et les deux poissons, et levant les yeux au ciel, il rendit grâces; et ayant rompu les pains, il les donna aux disciples, et les disciples les donnèrent au peuple.
20 Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
Tous en mangèrent, et furent rassasiés; et on emporta douze paniers pleins des morceaux qui restèrent.
21 Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
Et ceux qui avaient mangé étaient environ cinq mille hommes, sans compter les femmes et les petits enfants.
22 Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
Aussitôt après, Jésus obligea ses disciples à entrer dans la barque, et à passer avant lui de l'autre côté, pendant qu'il renverrait le peuple.
23 Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
Et après qu'il l'eut renvoyé, il monta sur la montagne, à part, pour prier; et le soir étant venu, il était là seul.
24 jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
Cependant la barque était déjà au milieu de la mer, battue des flots; car le vent était contraire.
25 Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
Et à la quatrième veille de la nuit, Jésus alla vers eux, marchant sur la mer.
26 Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
Et ses disciples, le voyant marcher sur la mer, furent troublés, et dirent: C'est un fantôme; et de la frayeur qu'ils eurent, ils crièrent.
27 Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
Mais aussitôt Jésus leur parla, et leur dit: Rassurez-vous; c'est moi, n'ayez point de peur.
28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
Et Pierre, répondant, lui dit: Seigneur! si c'est toi, ordonne que j'aille vers toi sur les eaux.
29 Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
Jésus lui dit: Viens. Et Pierre, étant descendu de la barque, marcha sur les eaux pour aller à Jésus.
30 Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
Mais, voyant que le vent était fort, il eut peur; et comme il commençait à enfoncer, il s'écria, et dit: Seigneur! Sauve-moi.
31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
Et aussitôt Jésus étendit la main, et le prit, lui disant: Homme de peu de foi, pourquoi as-tu douté?
32 Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
Et quand ils furent entrés dans la barque, le vent cessa.
33 Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
Alors ceux qui étaient dans la barque vinrent, et l'adorèrent, en disant: Tu es véritablement le Fils de Dieu.
34 Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
Et ayant passé le lac, ils vinrent dans le pays de Génézareth.
35 Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
Et quand les gens de ce lieu l'eurent reconnu, ils envoyèrent par toute la contrée d'alentour, et lui présentèrent tous les malades.
36 suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.
Et ils le priaient qu'ils pussent seulement toucher le bord de son habit; et tous ceux qui le touchèrent furent guéris.