< Mattiyu 14 >

1 A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
En ce temps-là, Hérode le tétrarque entendit parler de la renommée de Jésus;
2 sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
et il dit à ses serviteurs: C’est Jean le baptiseur; il est ressuscité des morts, et c’est pourquoi les miracles s’opèrent par lui.
3 To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
Car Hérode, ayant fait prendre Jean, l’avait fait lier et mettre en prison, à cause d’Hérodias, la femme de Philippe son frère;
4 gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
car Jean lui disait: Il ne t’est pas permis de l’avoir.
5 Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
Et tout en ayant le désir de le faire mourir, il craignait la foule, parce qu’ils le tenaient pour prophète.
6 A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
Mais lorsqu’on célébrait l’anniversaire de la naissance d’Hérode, la fille d’Hérodias dansa devant tous, et plut à Hérode:
7 har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
sur quoi il lui promit avec serment de lui donner tout ce qu’elle demanderait.
8 Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
Et elle, poussée par sa mère: Donne-moi ici, dit-elle, dans un plat, la tête de Jean le baptiseur.
9 Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
Et le roi en fut affligé; mais, à cause des serments et de ceux qui étaient à table avec lui, il donna l’ordre qu’on la lui donne.
10 ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
Et il envoya décapiter Jean dans la prison.
11 Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
Et sa tête fut apportée dans un plat et donnée à la jeune fille; et elle la porta à sa mère.
12 Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
Et ses disciples vinrent et enlevèrent le corps et l’ensevelirent; et s’en allant, ils rapportèrent à Jésus [ce qui était arrivé].
13 Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
Et Jésus, l’ayant entendu, se retira de là dans un bateau en un lieu désert, à l’écart; et les foules, l’ayant appris, le suivirent à pied, des [différentes] villes.
14 Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
Et étant sorti, il vit une grande foule; et il fut ému de compassion envers eux, et il guérit leurs infirmes.
15 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
Et le soir étant venu, ses disciples vinrent à lui, disant: Le lieu est désert, et l’heure est déjà passée; renvoie les foules, afin qu’elles s’en aillent aux villages et qu’elles s’achètent des vivres.
16 Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
Mais Jésus leur dit: Il n’est pas nécessaire qu’elles s’en aillent; vous, donnez-leur à manger.
17 Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
Mais ils lui disent: Nous n’avons ici que cinq pains et deux poissons.
18 Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
Et il dit: Apportez-les-moi ici.
19 Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
Et ayant donné l’ordre aux foules de s’asseoir sur l’herbe, ayant pris les cinq pains et les deux poissons, il regarda vers le ciel et bénit; et ayant rompu les pains, il les donna aux disciples, et les disciples aux foules.
20 Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
Et ils mangèrent tous et furent rassasiés. Et ils ramassèrent, des morceaux qui étaient de reste, douze paniers pleins.
21 Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
Or ceux qui avaient mangé étaient environ 5 000 hommes, outre les femmes et les enfants.
22 Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
Et aussitôt il contraignit les disciples de monter dans le bateau et de le précéder à l’autre rive, jusqu’à ce qu’il ait renvoyé les foules.
23 Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
Et quand il eut renvoyé les foules, il monta sur une montagne à l’écart pour prier; et le soir étant venu, il était là seul.
24 jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
Or le bateau était déjà au milieu de la mer, battu par les vagues, car le vent était contraire.
25 Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
Et à la quatrième veille de la nuit, il s’en alla vers eux, marchant sur la mer.
26 Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
Et les disciples, le voyant marcher sur la mer, furent troublés, disant: C’est un fantôme. Et ils crièrent de peur.
27 Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
Mais Jésus leur parla aussitôt, disant: Ayez bon courage; c’est moi, n’ayez point de peur.
28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
Et Pierre, lui répondant, dit: Seigneur, si c’est toi, commande-moi d’aller à toi sur les eaux.
29 Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
Et il dit: Viens. Et Pierre, étant descendu du bateau, marcha sur les eaux pour aller à Jésus.
30 Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
Mais voyant que le vent était fort, il eut peur; et comme il commençait à enfoncer, il s’écria, disant: Seigneur, sauve-moi!
31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
Et aussitôt Jésus, étendant la main, le prit et lui dit: Homme de petite foi, pourquoi as-tu douté?
32 Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
Et quand ils furent montés dans le bateau, le vent tomba.
33 Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
Et ceux qui étaient dans le bateau vinrent et lui rendirent hommage, disant: Véritablement tu es le Fils de Dieu!
34 Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
Et ayant passé à l’autre rive, ils vinrent dans la contrée de Génésareth.
35 Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
Et les hommes de ce lieu-là, l’ayant reconnu, envoyèrent dans tout le pays d’alentour; et on lui apporta tous ceux qui se portaient mal;
36 suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.
et ils le priaient de [les laisser] toucher seulement le bord de sa robe: et tous ceux qui le touchèrent furent complètement guéris.

< Mattiyu 14 >