< Mattiyu 14 >

1 A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
At that time, Herod the tetrarch heard the report concerning Yeshua,
2 sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
and said to his servants, “This is Yochanan the Immerser. He is risen from the dead. That is why these powers work in him.”
3 To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
For Herod had arrested Yochanan, bound him, and put him in prison for the sake of Herodias, his brother Philip’s wife.
4 gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
For Yochanan said to him, “It is not lawful for you to have her.”
5 Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
When he would have put him to death, he feared the multitude, because they counted him as a prophet.
6 A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
But when Herod’s birthday came, the daughter of Herodias danced among them and pleased Herod.
7 har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
Therefore he promised with an oath to give her whatever she should ask.
8 Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
She, being prompted by her mother, said, “Give me here on a platter the head of Yochanan the Immerser.”
9 Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
The king was grieved, but for the sake of his oaths and of those who sat at the table with him, he commanded it to be given,
10 ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
and he sent and beheaded Yochanan in the prison.
11 Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
His head was brought on a platter and given to the young lady; and she brought it to her mother.
12 Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
His disciples came, took the body, and buried it. Then they went and told Yeshua.
13 Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
Now when Yeshua heard this, he withdrew from there in a boat to a deserted place apart. When the multitudes heard it, they followed him on foot from the cities.
14 Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
Yeshua went out, and he saw a great multitude. He had compassion on them and healed their sick.
15 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
When evening had come, his disciples came to him, saying, “This place is deserted, and the hour is already late. Send the multitudes away, that they may go into the villages, and buy themselves food.”
16 Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
But Yeshua said to them, “They don’t need to go away. You give them something to eat.”
17 Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
They told him, “We only have here five loaves and two fish.”
18 Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
He said, “Bring them here to me.”
19 Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
He commanded the multitudes to sit down on the grass; and he took the five loaves and the two fish, and looking up to heaven, he blessed, broke and gave the loaves to the disciples; and the disciples gave to the multitudes.
20 Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
They all ate and were filled. They took up twelve baskets full of that which remained left over from the broken pieces.
21 Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
Those who ate were about five thousand men, in addition to women and children.
22 Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
Immediately Yeshua made the disciples get into the boat and go ahead of him to the other side, while he sent the multitudes away.
23 Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
After he had sent the multitudes away, he went up into the mountain by himself to pray. When evening had come, he was there alone.
24 jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
But the boat was now in the middle of the sea, distressed by the waves, for the wind was contrary.
25 Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
In the fourth watch of the night, Yeshua came to them, walking on the sea.
26 Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
When the disciples saw him walking on the sea, they were troubled, saying, “It’s a ghost!” and they cried out for fear.
27 Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
But immediately Yeshua spoke to them, saying, “Cheer up! It is I! Don’t be afraid.”
28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
Peter answered him and said, “Lord, if it is you, command me to come to you on the waters.”
29 Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
He said, “Come!” Peter stepped down from the boat and walked on the waters to come to Yeshua.
30 Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
But when he saw that the wind was strong, he was afraid, and beginning to sink, he cried out, saying, “Lord, save me!”
31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
Immediately Yeshua stretched out his hand, took hold of him, and said to him, “You of little faith, why did you doubt?”
32 Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
When they got up into the boat, the wind ceased.
33 Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
Those who were in the boat came and worshiped him, saying, “You are truly the Son of God!”
34 Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
When they had crossed over, they came to the land of Gennesaret.
35 Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
When the people of that place recognized him, they sent into all that surrounding region and brought to him all who were sick;
36 suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.
and they begged him that they might just touch the fringe of his garment. As many as touched it were made whole.

< Mattiyu 14 >