< Mattiyu 14 >

1 A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
At that time Herod the tetrarch heard of the fame of Jesus,
2 sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
and said to his servants, This is John the Baptist; he hath risen from the dead, and therefore do these powers work in him.
3 To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
For Herod had seized John, and bound him, and put him in prison, on account of Herodias, his brother Philip's wife.
4 gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
For John said to him, It is not lawful for thee to have her.
5 Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
And wishing to put him to death, he feared the multitude, because they regarded him as a prophet.
6 A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
But when Herod's birthday was kept, the daughter of Herodias danced before them, and pleased Herod;
7 har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
whereupon he promised with an oath to give her whatever she might ask.
8 Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
And she, being set on by her mother, saith, Give me here on a platter the head of John the Baptist.
9 Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
And the king was sorry; but on account of his oaths, and of those at table with him, he ordered it to be given,
10 ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
and sent and beheaded John in the prison.
11 Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
And his head was brought on a platter, and given to the damsel; and she brought it to her mother.
12 Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
And his disciples came and took up the body, and buried it, and went and told Jesus.
13 Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
When Jesus heard of it, he withdrew thence in a boat into a desert place apart; and the multitudes hearing of it followed him on foot from the cities.
14 Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
And when he came forth he saw a great multitude; and he was moved with compassion for them, and healed their sick.
15 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
And when it was evening, the disciples came to him, saying, This is a desert place, and it is now late; send the multitudes away therefore, that they may go to the villages and buy themselves victuals.
16 Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
But he said to them, They need not go away; do ye give them food.
17 Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
And they say to him, We have here only five loaves, and two fishes.
18 Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
He said, Bring them hither to me.
19 Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
And bidding the multitudes to lie down on the grass, he took the five loaves and the two fishes, and, looking up to heaven, he blessed; and having broken the loaves he gave them to his disciples, and the disciples to the multitudes.
20 Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
And they all ate, and were filled. And they took up of the fragments that remained, twelve baskets full.
21 Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
And they who ate were about five thousand men, besides women and children.
22 Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
and he constrained the disciples to get into the boat, and to go before him to the other side, while he sent the multitudes away.
23 Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
And when he had sent the multitudes away, he went up into the mountain apart to pray. And when evening came, he was there alone.
24 jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
But the boat was now in the midst of the lake, tossed by the waves; for the wind was contrary.
25 Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
And in the fourth watch of the night, he went to them, walking on the lake.
26 Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
And seeing him walking on the lake, they were dismayed, saying, It is a spectre; and they cried out for fear.
27 Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
But he immediately spoke to them, saying, Be of good cheer, it is I; be not afraid.
28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
And Peter answering him said, Lord, if it be thou, bid me come to thee on the water.
29 Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
And he said, Come. And Peter, coming down from the boat, walked on the water, and came to Jesus.
30 Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
But seeing the wind, he was afraid; and beginning to sink, he cried out, saying, Lord, save me!
31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
And Jesus immediately stretched out his hand, and took hold of him, and said to him, Thou of little faith, why didst thou doubt?
32 Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
And when they had got into the boat, the wind ceased.
33 Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
And they that were in the boat fell down before him, saying, Truly thou art the Son of God.
34 Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
And crossing over, they came to land, to Gennesaret.
35 Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
And the men of that place, when they saw who he was, sent out into all that country round, and brought to him all the diseased,
36 suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.
and besought him that they might only touch the fringe of his garment; and as many as touched were made well.

< Mattiyu 14 >