< Mattiyu 14 >
1 A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
At that time Herod the tetrarch heard of the fame of Jesus;
2 sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
and he said to his servants: This is John The Immerser; he has risen from the dead; and for this reason the powers of the spiritual world are active within him.
3 To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
For Herod had laid hold of John, and bound him, and put him in prison on account of Herodias, the wife of his brother Philip.
4 gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
For John said to him: It is not lawful for you to have her.
5 Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
And he intended to put him to death, but feared the multitude, because they regarded him as a prophet.
6 A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
But when Herod’s birthday was kept, the daughter of Herodias danced in the midst, and pleased Herod.
7 har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
Wherefore he promised, with an oath, to give her whatever she would ask.
8 Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
And being previously instigated by her mother, she said: Give me here in a dish the head of John the Immerser?
9 Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
And the king was grieved: but on account of his oath, and those who reclined at table with him, he commanded it to be given.
10 ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
And he sent and beheaded John in the prison.
11 Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
And his head was brought in a dish, and given to the maiden: and she carried it to her mother.
12 Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
And his disciples came and took away the body, and buried it; and went and told Jesus.
13 Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
And when Jesus heard of it, he withdrew from that place, by ship, into a desert place apart: and the multitudes, when they heard of his departure, followed him, on foot, from the cities.
14 Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
And when Jesus came out, he saw a great multitude, and was moved with compassion for them, and cured their sick.
15 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
And when it was evening, his disciples came to him, and said: This is a desert place, and the hour is now past; send the multitudes away, that they may go into the villages, and buy themselves food.
16 Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
But Jesus said to them: They need not go away; do you give them food.
17 Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
They said to him: We have here but five loaves and two fishes.
18 Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
He said: Bring them hither to me.
19 Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
And he commanded the multitudes to recline upon the grass: and he took the five loaves and the two fishes, and looked up to heaven, and blessed, and broke, and gave the bread to the disciples, and the disciples gave it to the multitudes.
20 Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
And they all ate and were satisfied. And they took up what remained of the broken pieces, twelve baskets full.
21 Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
And they that had eaten were about five thousand men, besides women and children.
22 Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
And he immediately constrained his disciples to get into the ship, and go before him to the opposite side, while he sent the multitudes away.
23 Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
And when he had sent the multitudes away, he went up into the mountain apart to pray. And when evening came, he was there alone.
24 jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
But the ship was now in the midst of the sea, tossed by the waves, for the wind was against them.
25 Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
And in the fourth watch of the night he came to them, walking on the sea.
26 Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
And when the disciples saw him walking on the sea, they were alarmed, and said: It is a specter! and they cried out for fear.
27 Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
But Jesus immediately spoke to them, and said: Take courage; it is I; be not afraid.
28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
And Peter answered him, and said: Lord, if it be thou, bid me come to thee on the water.
29 Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
And he said: Come. And Peter went down from the ship, and walked upon the water to go to Jesus.
30 Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
But when he saw the wind strong, he was afraid; and beginning to sink, he cried out, saying: Lord, save me.
31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
And Jesus immediately stretched out his hand, and took hold of him, and said to him: O you of little faith, why did you doubt?
32 Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
And when they had entered the ship, the wind ceased.
33 Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
And they that were in the ship came and worshiped him, saying: Truly, thou art the Son of God.
34 Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
And when they had passed over, they came into the land of Gennesaret.
35 Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
And when the men of that place had knowledge of him, they sent out into all the neighboring country, and brought to him all that were sick;
36 suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.
and besought him that they might only touch the fringe of his mantle; and as many as touched were perfectly saved.