< Mattiyu 13 >
1 A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin.
В день же той изшед Иисус из дому, седяше при мори.
2 Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci.
И собрашася к Нему народи мнози, якоже Ему в корабль влезти и сести: и весь народ на брезе стояше.
3 Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
И глагола им притчами много, глаголя: се, изыде сеяй, да сеет:
4 Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su.
и сеющу ему, ова падоша при пути, и приидоша птицы и позобаша я:
5 Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi.
другая же падоша на каменных, идеже не имеяху земли многи, и абие прозябоша, зане не имеяху глубины земли:
6 Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai.
солнцу же возсиявшу присвянуша, и зане не имеяху корения, изсхоша:
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su.
другая же падоша в тернии, и взыде терние и подави их:
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka.
другая же падоша на земли добрей и даяху плод, ово убо сто, ово же шестьдесят, ово же тридесять:
9 Duk mai kunnen ji, yă ji.”
имеяй ушы слышати да слышит.
10 Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”
И приступивше ученицы (Его) рекоша Ему: почто притчами глаголеши им?
11 Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba.
Он же отвещав рече им: яко вам дано есть разумети тайны Царствия Небеснаго, онем же не дано есть:
12 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe.
иже бо имать, дастся ему и преизбудет (ему): а иже не имать, и еже имать, возмется от него:
13 Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan. “Ko da yake suna kallo, ba sa gani; ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.
сего ради в притчах глаголю им, яко видяще не видят, и слышаще не слышат, ни разумеют:
14 A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, “‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba; za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
и сбывается в них пророчество Исаиино, глаголющее: слухом услышите, и не имате разумети: и зряще узрите, и не имате видети:
15 Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
отолсте бо сердце людий сих, и ушима тяжко слышаша, и очи свои смежиша, да не когда узрят очима, и ушима услышат, и сердцем уразумеют, и обратятся, и изцелю их.
16 Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji.
Ваша же блаженна очеса, яко видят, и уши ваши, яко слышат:
17 Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.
аминь бо глаголю вам, яко мнози пророцы и праведницы вожделеша видети, яже видите, и не видеша, и слышати, яже слышите, и не слышаша.
18 “To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan.
Вы же услышите притчу сеющаго:
19 Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya.
всякому слышащему слово Царствия и не разумевающу, приходит лукавый и восхищает всеянное в сердцы его: сие есть, еже при пути сеянное.
20 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna.
А на камени сеянное, сие есть слышай слово и абие с радостию приемлет е:
21 Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya.
не имать же корене в себе, но привременен есть: бывши же печали или гонению словесе ради, абие соблажняется.
22 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn )
А сеянное в тернии, се есть слышай слово, и печаль века сего и лесть богатства подавляет слово, и без плода бывает. (aiōn )
23 Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”
А сеянное на добрей земли, се есть слышай слово и разумевая: иже убо плод приносит и творит ово сто, ово же шестьдесят, ово тридесять.
24 Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa.
Ину притчу предложи им, глаголя: уподобися Царствие Небесное человеку, сеявшу доброе семя на селе своем:
25 Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa.
спящым же человеком, прииде враг его и всея плевелы посреде пшеницы и отиде:
26 Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.
егда же прозябе трава и плод сотвори, тогда явишася и плевелие.
27 “Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’
Пришедше же раби господина, реша ему: господи, не доброе ли семя сеял еси на селе твоем? Откуду убо имать плевелы?
28 “Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’ “Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’
Он же рече им: враг человек сие сотвори. Раби же реша ему: хощеши ли убо, да шедше исплевем я?
29 “Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar.
Он же рече (им): ни: да не когда восторгающе плевелы, восторгнете купно с ними (и) пшеницу:
30 Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’”
оставите расти обое купно до жатвы: и во время жатвы реку жателем: соберите первее плевелы и свяжите их в снопы, яко сожещи я: а пшеницу соберите в житницу мою.
31 Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa.
Ину притчу предложи им, глаголя: подобно есть Царствие Небесное зерну горушичну, еже взем человек всея на селе своем,
32 Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”
еже малейше убо есть от всех семен: егда же возрастет, более (всех) зелий есть и бывает древо, яко приити птицам небесным и витати на ветвех его.
33 Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”
Ину притчу глагола им: подобно есть Царствие Небесное квасу, егоже вземши жена скры в сатех триех муки, дондеже вскисоша вся.
34 Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai.
Сия вся глагола Иисус в притчах народом, и без притчи ничесоже глаголаше к ним:
35 Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa, “Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”
яко да сбудется реченное пророком, глаголющим: отверзу в притчах уста Моя: отрыгну сокровенная от сложения мира.
36 Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”
Тогда оставль народы, прииде в дом Иисус. И приступиша к Нему ученицы Его, глаголюще: скажи нам притчу плевел селных.
37 Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum.
Он же отвещав рече им: сеявый доброе семя есть Сын Человеческий:
38 Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne’ya’yan mugun nan,
а село есть мир: доброе же семя, сии суть сынове Царствия, а плевелие суть сынове неприязненнии:
39 abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn )
а враг всеявый их есть диавол: а жатва кончина века есть: а жатели Ангели суть. (aiōn )
40 “Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn )
Якоже убо собирают плевелы и огнем сожигают, тако будет в скончание века сего: (aiōn )
41 Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
послет Сын Человеческий Ангелы Своя, и соберут от Царствия Его вся соблазны и творящих беззаконие
42 Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
и ввергут их в пещь огненну: ту будет плачь и скрежет зубом:
43 Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”
тогда праведницы просветятся яко солнце в Царствии Отца их. Имеяй ушы слышати да слышит.
44 “Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
Паки подобно есть Царствие Небесное сокровищу сокровену на селе, еже обрет человек скры, и от радости его идет, и вся, елика имать, продает, и купует село то.
45 “Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau.
Паки подобно есть Царствие Небесное человеку купцу, ищущу добрых бисерей,
46 Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
иже обрет един многоценен бисер, шед продаде вся, елика имяше, и купи его.
47 “Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri.
Паки подобно есть Царствие Небесное неводу ввержену в море и от всякаго рода собравшу,
48 Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau.
иже егда исполнися, извлекоша и на край, и седше избраша добрыя в сосуды, а злыя извергоша вон.
49 Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn )
Тако будет в скончание века: изыдут Ангели, и отлучат злыя от среды праведных, (aiōn )
50 su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
и ввергут их в пещь огненную: ту будет плачь и скрежет зубом.
51 Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?” Suka amsa, “I.”
Глагола им Иисус: разуместе ли сия вся? Глаголаша Ему: ей, Господи.
52 Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”
Он же рече им: сего ради всяк книжник, научився Царствию Небесному, подобен есть человеку домовиту, иже износит от сокровища своего новая и ветхая.
53 Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can.
И бысть, егда сконча Иисус притчи сия, прейде оттуду.
54 Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka?
И пришед во отечествие Свое, учаше их на сонмищи их, яко дивитися им и глаголати: откуду Сему премудрость сия и силы?
55 Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu,’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba?
Не Сей ли есть тектонов сын? Не Мати ли Его нарицается Мариам, и братия Его Иаков и Иосий, и Симон и Иуда?
56 Duk’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?”
И сестры Его не вся ли в нас суть? Откуду убо Сему сия вся?
57 Sai suka ji haushinsa. Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”
И блажняхуся о Нем. Иисус же рече им: несть пророк без чести, токмо во отечествии своем и в дому своем.
58 Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.
И не сотвори ту сил многих за неверство их.