< Mattiyu 13 >

1 A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin.
И онај дан изишавши Исус из куће сеђаше крај мора.
2 Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci.
И сабраше се око Њега људи многи, тако да мора ући у лађу и сести; а народ сав стајаше по брегу.
3 Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
И Он им казива много у причама говорећи: Гле, изиђе сејач да сеје.
4 Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su.
И кад сејаше, једна зрна падоше крај пута, и дођоше птице и позобаше их;
5 Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi.
А друга падоше на каменита места, где не беше много земље, и одмах изникоше; јер не беше у дубину земље.
6 Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai.
И кад обасја сунце, повенуше, и будући да немаху жила, посахнуше.
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su.
А друга падоше у трње, и нарасте трње, и подави их.
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka.
А друга падоше на земљу добру, и доношаху род, једно по сто, а једно по шездесет, а једно по тридесет.
9 Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Ко има уши да чује нека чује.
10 Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”
И приступивши ученици рекоше Му: Зашто им говориш у причама?
11 Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba.
А Он одговарајући рече им: Вама је дано да знате тајне царства небеског, а њима није дано.
12 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe.
Јер ко има, даће му се, и претећи ће му; а који нема, узеће му се и оно што има.
13 Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan. “Ko da yake suna kallo, ba sa gani; ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.
Зато им говорим у причама, јер гледајући не виде, и чујући не чују нити разумеју.
14 A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, “‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba; za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
И збива се на њима пророштво Исаијино, које говори: Ушима ћете чути, и нећете разумети; и очима ћете гледати, и нећете видети.
15 Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
Јер је одрвенило срце ових људи, и ушима тешко чују, и очи су своје затворили да како не виде очима, и ушима не чују, и срцем не разумеју, и не обрате се да их исцелим.
16 Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji.
А благо вашим очима што виде, и ушима вашим што чују.
17 Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.
Јер вам кажем заиста да су многи пророци и праведници желели видети шта ви видите, и не видеше; и чути шта ви чујете, и не чуше.
18 “To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan.
Ви пак чујте причу о сејачу:
19 Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya.
Свакоме који слуша реч о царству и не разуме, долази нечастиви и краде посејано у срцу његовом: то је око пута посејано.
20 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna.
А на камену посејано то је који слуша реч и одмах с радости прими је,
21 Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya.
Али нема корена у себи, него је непостојан, па кад буде до невоље или га потерају речи ради, одмах удари натраг.
22 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn g165)
А посејано у трњу то је који слуша реч, но брига овог света и превара богатства загуше реч, и без рода остане. (aiōn g165)
23 Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”
А посејано на доброј земљи то је који слуша реч и разуме, који дакле и род рађа, и доноси један по сто, а један по шездесет, а један по тридесет.
24 Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa.
Другу причу каза им говорећи: Царство је небеско као човек који посеја добро семе у пољу свом,
25 Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa.
А кад људи поспаше, дође његов непријатељ и посеја кукољ по пшеници, па отиде.
26 Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.
А кад ниче усев и род донесе, онда се показа кукољ.
27 “Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’
Тада дођоше слуге домаћинове и рекоше му: Господару! Ниси ли ти добро семе сејао на својој њиви? Откуда дакле кукољ?
28 “Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’ “Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’
А он рече им: Непријатељ човек то учини. А слуге рекоше му: Хоћеш ли дакле да идемо да га почупамо?
29 “Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar.
А он рече: Не; да не би чупајући кукољ почупали заједно с њиме пшеницу.
30 Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’”
Оставите нека расте обоје заједно до жетве; и у време жетве рећи ћу жетеоцима: Саберите најпре кукољ, и свежите га у снопље да га сажежем; а пшеницу свезите у житницу моју.
31 Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa.
Другу причу каза им говорећи: Царство је небеско као зрно горушичино које узме човек и посеје на њиви својој,
32 Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”
Које је истина најмање од свију семена, али кад узрасте, веће је од свега поврћа, и буде дрво да птице небеске долазе, и седају на његовим гранама.
33 Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”
Другу причу каза им: Царство је небеско као квасац који узме жена и метне у три копање брашна док све не ускисне.
34 Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai.
Све ово у причама говори Исус људима, и без приче ништа не говораше им:
35 Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa, “Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”
Да се збуде шта је казао пророк говорећи: Отворићу у причама уста своја, казаћу сакривено од постања света.
36 Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”
Тада остави Исус људе, и дође у кућу. И приступише к Њему ученици Његови говорећи: Кажи нам причу о кукољу на њиви.
37 Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum.
А Он одговарајући рече им: Који сеје добро семе оно је Син човечији;
38 Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne’ya’yan mugun nan,
А њива је свет; а добро семе синови су царства, а кукољ синови су зла;
39 abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn g165)
А непријатељ који га је посејао јесте ђаво; а жетва је последак овог века; а жетеоци су анђели. (aiōn g165)
40 “Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn g165)
Као што се дакле кукољ сабира, и огњем сажиже, тако ће бити на крају овог века. (aiōn g165)
41 Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
Послаће Син човечији анђеле своје, и сабраће из царства Његовог све саблазни и који чине безакоње.
42 Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
И бациће их у пећ огњену: онде ће бити плач и шкргут зуба.
43 Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Тада ће се праведници засјати као сунце у царству Оца свог. Ко има уши да чује нека чује.
44 “Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
Још је царство небеско као благо сакривено у пољу, које нашавши човек сакри и од радости зато отиде и све што има продаде и купи поље оно.
45 “Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau.
Још је царство небеско као човек трговац који тражи добар бисер,
46 Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
Па кад нађе једно многоцено зрно бисера, отиде и продаде све што имаше и купи га.
47 “Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri.
Још је царство небеско као мрежа која се баци у море и заграби од сваке руке рибе;
48 Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau.
Која кад се напуни, извукоше је на крај, и седавши, избраше добре у судове, а зле бацише напоље.
49 Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn g165)
Тако ће бити на полетку века: изићи ће анђели и одлучиће зле од праведних. (aiōn g165)
50 su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
И бациће их у пећ огњену: онде ће бити плач и шкргут зуба.
51 Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?” Suka amsa, “I.”
Рече им Исус: Разуместе ли ово? Рекоше Му: Да, Господе.
52 Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”
А Он им рече: Зато је сваки књижевник који се научио царству небеском као домаћин који износи из клети своје ново и старо.
53 Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can.
И кад сврши Исус приче ове, отиде оданде.
54 Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka?
И дошавши на постојбину своју, учаше их по зборницама њиховим тако да Му се дивљаху, и говораху: Откуд овоме премудрост ова и моћи?
55 Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu,’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba?
Није ли ово дрводељин син? Не зове ли се мати његова Марија, и браћа његова Јаков, и Јосија, и Симон, и Јуда?
56 Duk’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?”
И сестре његове нису ли све код нас? Откуд њему ово све?
57 Sai suka ji haushinsa. Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”
И саблажњаваху се о Њега. А Исус рече им: Нема пророка без части осим на постојбини својој и у дому свом.
58 Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.
И не створи онде чудеса многих за неверство њихово.

< Mattiyu 13 >