< Mattiyu 13 >
1 A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin.
Uluhiku nulanso u Yesu akahega kitalakwe akikie pampelo a luzi.
2 Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci.
Milundo ukulu ukilingiila kuligitya nung'wenso, akingila mibini akikie, milundo wihi ukimika pa mpelo a luzi.
3 Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
Sunga u Yesu akaligitya kwa mpyani, Goza, mutemeli aiwendile temela.
4 Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su.
Naukutemela imbeu ing'wi ikagwa mumpelo mpelo anzila inyunyi ikahoela.
5 Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi.
Ning'wi ikagwa migwe, singaikapata imahalu. Ikakaya kuheluka kunsoko mahalu aimakehu.
6 Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai.
Ingigwa ilyoa nailatoroka ikasonswa nsoko aingila nga mili hangi ikuma.
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su.
Imbeu ing'wi ikagwa mumija. Imiti nikite imiija ikalipa migula ikatunyiilya.
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka.
Mbeu ing'wi ikagwa mumahalu ni maza, ikatuga mbeu, ning'wi ikakila igana ling'wi, ning'wi makumi mutandatu, ning'wi makumi atatu.
9 Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Nukete iakutwi ije.
10 Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”
Iamanyisigwa akwe akaza akamukolya niki nukendaligitya kukiila mpyani?
11 Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba.
U Yesu akasukiilya akaila, lumbi nimpewe kulinga inkunku wa kigulu ianyu singa apewe.
12 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe.
Kululo uyu nutite ukangeeligwa hangi uyu numugila ukuhegeligwa kaniki nazutite.
13 Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan. “Ko da yake suna kallo, ba sa gani; ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.
Ingi kuligitya nienso kua mpyani ingi nsoko akuona, aleke kuona itai, ataizeazija aleke kija nukulinga.
14 A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, “‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba; za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
Uunyakidagu wang'wa Isaya wakondanila kitalao, nuuliye kija mukija singamkulinga kugoza mukugoza shamukuona.
15 Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
Inkolo ya antu awa ikoli mukiti, ikakukija, imiho ao akunikiwe, aleke kuona na miho ao, nukija kua kutwe ao, nukulinga kwa nkolo yao, kululo anga aiampilukile hangi anzeaguna.”
16 Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji.
Kululo gwa imiho anyu akembetilwe, nsoko akuona, niakutwe anyu akija.
17 Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.
Tai kumuila, anyakidagu idu niaantu niatai akete insula akuona inkani izi nimukuiona, shaikahuma kuona, ailoilwe kija aya nimendija shaikija.
18 “To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan.
Ingi tegeeli impyani amutemeli.
19 Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya.
Uyu nuija ulukani nulautemi wa kigulu ahite kulinga, hapo umubi wiza hola iko nikitemiwe munkolo akwe. Iye yiyi mbeu nitemewe munzila.
20 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna.
Uyu nutemewe migwe yuyu nuikaya kija nukusingiilya kua ulowa.
21 Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya.
Iza akili mugila anga mili, wigimya matungo makehu. Anga hangwe ni nkani ni nkaku wikaya kugwa.
22 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn )
Uyu nautemewe mumiti na mija yuyu nuwija ulukani, kunu akazutyatile makani umunkumbigulu akalutunyiilya ulukani lang'wi Tunda lakahita kuluga indya ninza. (aiōn )
23 Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”
Nautemewe mumahalu nimaza, yuyu nuija ulukani nukulija, nukululinga. Uyu yuyu nuituga indya, nukulongoleka kutuga kukila igana ling'wi ning'wi makumi atatu.”
24 Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa.
U Yesu akaapa mpyani ngiza. Akalunga, utemi wa kigulu wimpyanigwe numuntu nautemee imbeu mumugunda wakwe.
25 Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa.
Iantu naiatindila umulugu akaza akatemela iapungu pakati a ngano sunga akalongola yakwe.
26 Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.
Ingano nakonda kupuma nukupumya indya yakwe, nia pungu akigela hangi.
27 “Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’
Itumi amumugunda akaza akamukolya shautemee ne imbeu ni nza mumugunda wako? Latula ule gwa likite apungu?
28 “Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’ “Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’
Akaila mulugu witumile iti. Eitumi ikamuila iti gwa utakila kende kumipe?
29 “Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar.
Umukola mugunda angalunge, aa imatungo nimukipa iapungu mukipa palung'wi ni ngano.
30 Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’”
Maleki akule palung'wi sunga imatungo akuogola kuligitya kuagoli ipi iapungu mutunge mapanzi mapunzi mumasonse ingano milingiile misalanka lane.”
31 Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa.
Hangi u Yesu akaapumilya mpyani ngiza akalunga, utemi wa kigulu wimpyani ni mbeu a haladali iyi nu muntu auhoile akatemela mumugunda wakwe.
32 Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”
Imbeu iyi tai niino kukila mbeu yihi ninino. Kululo ilungile ikulu kukila indya yihi niambustani, ukutula mti, kina ni nyuni iziza tula zenga niitie mumatambi akwe.”
33 Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”
Akaaila mpyani ngiza hangi, “Utemi wa kigulu anga igai naihoilwe numusungu nukuhalinkanya ininoinino itatu nia utu mpaka witikiilye.
34 Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai.
Aya hii u Yesu akauila umilundo kukiila mpyani, inkani yihi aiwiiligitya kukiila mpyani.
35 Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa, “Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”
Iki aitule kina iko naikakondigwe kuligitigwa kukiila anyakidagu kihuma kipika apo naulungile kulugula ikimilo kane kwa mpyani, kuligitya ihi ayo napikilwe kupuma ung'wando wa unkumbigulu.”
36 Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”
Sunga u Yesu akauleka umilundo akalongola kitalakwe. Iamanyisigwa akue akamutyata akalunga, kutemanuilye impyani iyi naapungu mumugunda.”
37 Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum.
U Yesu akasisha akalunga, Nuitemela imbeu ninza ingi ng'wana wang'wa Adamu.
38 Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne’ya’yan mugun nan,
Umugunda unkumbigulu, ni mbeu ninza awa ana autemi. Iapungu ana ang'wa uyo numubi, nimbeu izi nuitemee mulugu.
39 abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn )
Nuogoli mpelu aunkumbigulu niaogoli ia malaika. (aiōn )
40 “Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn )
Anga iapungu niilingiilwa nukusonswa umoto. Iti uu izitula mpelu aunkumbigulu. (aiōn )
41 Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
Ung'wana wang'wa Adamu ukualagiilya iamalaika akwe, hangi ukilingiila kupuma muutemi wakwe ni nkani yihi nailetekeye imilandu nawa ihi niituma uubi.
42 Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
Akuaguma ihi milungu la moto, kung'wanso kizeze kikoli kililo nikakusia na mino.
43 Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Pang'wanso iantu niatai azizemili ginta anga ilyoa muutemi wang'wa tata wao. Uyu nukete iakutwe nije.
44 “Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
Uutemi wa kigulu wa hanga anga ikiuto nikipihilwe mumugunda. Umuntu akaona akakipiha mulumbili wakwe akalongola kugulya ihi nautite akaugule umugunda.
45 “Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau.
Hangi uutemi wa kigulu wihanga anga umuntu numusuluja nuipenza insao.
46 Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
Matungo naiwamiona insao, akalongola akagulya ihi nautite, akamigula.
47 “Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri.
Uutemi wa kigulu wili anga inyavu nikoli muluzi, ni liingiila kila ikintu.
48 Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau.
Naizula inyavu ikamuluta kumpelo. Sunga akikie pihi akiliingila imaintu nimaza muiseme, nishanganzinza ikagungwa kuli.
49 Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn )
Izizatula iti kumpolo ihi, aziza kumutemanula muantu niabi, kupuma muantu nia tai. (aiōn )
50 su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
Nukuaguma milungu la moto, kung'wanso izize ukoli uhungeelya wa kusiana mino.
51 Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?” Suka amsa, “I.”
Malinga ne aya ihi? Iamanyisigwa ikalunga “Kalinga.”
52 Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”
Sunga u Yesu akaila, muika nkani wihi nuatula mumanyisigwa wa utemi wimpyani numukolo nyumba nuipumya ikiuto kwakwe nikamaintu ni nimapya naya nakali.
53 Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can.
Ikatula u Yesu naiwakondya kupumya impyani yihi, akahega kung'wanso.
54 Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka?
Sunga u Yesu akapika mukisali kakwe, akutula amanyisa iantu mumatekeelo, ingi gwa ikakuilwa ikalunga, umuntu yu auhoe pi u hugu wuu nukuilwa uwu?
55 Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu,’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba?
Umuntu singa ng'wana wang'wa mutamula mbao? U Mariamu singa nyinya? Nianyandugu singa Yakobo, Yusufu, Simoni nu Yuda?
56 Duk’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?”
Nialuna akwe kuwatite apa pitaitu? Umuntu uyu umahoeepi aya hii?
57 Sai suka ji haushinsa. Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”
Akaatasha sunga u Yesu akaila, umunyakidagu shanga wiulya ikulyo kuleka kitalao nukihi nao.
58 Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.
Singa akahuma kituma ukuuilwa nuidu kunsoko aiagila anga uhuili nung'wenso.