< Mattiyu 13 >

1 A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin.
On that day, Jesus, going out of the house, was sitting near the sea:
2 Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci.
and there were gathered unto him, large multitudes, so that, he, into a boat, entered, and was sitting, and, all the multitude, on the beach was standing.
3 Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
And he spake unto them many things, in parables, saying: Lo! the sower went forth to sow, —
4 Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su.
and, as he sowed, some, indeed, fell by the pathway, and, the birds, came, and devoured it;
5 Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi.
And, some, fell on the rocky places, where it had not much earth, —and, straightway, it sprang up, because if had no depth of earth;
6 Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai.
and, the sun arising, it was scorched, and, because it had no root, it withered away;
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su.
And, some, fell upon the thorns, and the thorns came up, and choked it;
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka.
But, some, fell upon the good ground, and did yield fruit, —this, indeed a hundred fold, and, that, sixty, and, the other, thirty.
9 Duk mai kunnen ji, yă ji.”
He that hath ears, let him hear.
10 Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”
And the disciples, coming near, said to him, Wherefore, in parables, art thou speaking to them?
11 Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba.
And, he, answering, said, Because, unto you, hath it been given, to get to know the sacred secrets of the kingdom of the heavens, —whereas, unto them, hath it not been given.
12 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe.
For, whosoever hath, it shall be given, to him, and he shall be made to abound, —but, whoever hath not, even what he hath, shall be taken from him?
13 Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan. “Ko da yake suna kallo, ba sa gani; ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.
For this reason, in parables, unto them, do I speak, —because, seeing, they see not, and, hearing, they hear not, —neither do they understand.
14 A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, “‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba; za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
And, again is being fulfilled in them, the prophecy of Isaiah, which saith, —They shall, surely hear, and yet will not understand, and, surely see, and yet not perceive;
15 Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
For the heart of this people hath become dense, and, with their ears, heavily have they heard, and, their eyes, have they closed, —lest, once they should see with their eyes, and, with their ears, should hear, and, with their hearts, should understand, and return; when I would certainly heal them.
16 Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji.
But happy are, your, eyes, that they see, and your ears, that they hear;
17 Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.
For, verily, I say unto you—Many prophets and righteous men, have coveted to see what ye see, and have not seen, and to hear what ye hear, and have not heard.
18 “To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan.
Hear, ye, then, the parable of him that sowed: —
19 Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya.
When anyone heareth the word of the kingdom, and understandeth it not, the wicked one cometh, and catcheth up that which hath been sown in his heart, —this, is he, by the pathway, sown.
20 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna.
And, he on the rocky places sown, the same, is he that, heareth the word, and, straightway, with joy, receiveth it;
21 Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya.
yet hath he no root in himself, but is, only for a season, —and, there arising, tribulation or persecution because of the word, straightway, he findeth cause of stumbling.
22 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn g165)
And, he among the thorns sown, the same, is he that, heareth the word, —and, the anxiety of the age and the deceit of riches, choke up the word, and, unfruitful, it becometh. (aiōn g165)
23 Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”
But, he on the good ground sown, the same, is he who doth hear and understand the word, who, indeed, beareth fruit and produceth, —this, a hundred, and, that, sixty, and, the other, thirty.
24 Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa.
Another parable, put he before them, saying—The kingdom of the heavens hath become like a man sowing good seed in his field;
25 Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa.
and, while men were sleeping, his enemy came, and sowed over darnel, in among the wheat, —and away he went.
26 Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.
And, when the blade shot up, and brought forth, fruit, then, appeared, the darnel also.
27 “Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’
And the servants of the householder, coming near, said to him, —Sir! was it not, good seed, thou didst sow in thy field? Whence then hath it, darnel?
28 “Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’ “Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’
And he said unto them—An enemy, hath, done this. And they say, unto him—Wilt thou, then, that we go and collect it?
29 “Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar.
And, he, saith—Nay! lest, at any time, while collecting the darnel, ye uproot, along with it, the wheat:
30 Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’”
Suffer both to grow together until the harvest, and at, harvest time, I will say unto the reapers, —Collect ye first, the darnel, and bind it into bundles, with a view to the burning it up; but, the wheat, be gathering it into my barn.
31 Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa.
Another parable, put he before them, saying—The kingdom of the heavens is like unto, a grain of mustard seed, which a man took and sowed in his field;
32 Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”
which, indeed, is, less, than all seeds, but, when grown, is greater than garden-plants, and becometh a tree, —so that the birds of heaven come, and lodge among its branches.
33 Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”
Another parable, [spake he unto them]: —The kingdom of the heavens is like, unto leaven, which a woman took and hid in three measures of flour until, the whole, was leavened.
34 Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai.
All these things, spake Jesus in parables, unto the multitudes, and, without a parable, was he speaking, nothing, unto them:
35 Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa, “Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”
that it might be fulfilled, which was spoken through the prophet, saying—I will open, in parables, my mouth, I will bring up things hidden from the foundation!
36 Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”
Then, dismissing the multitudes, he went into the house, and his disciples came near to him, saying—Make quite plain to us the parable of the darnel of the field.
37 Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum.
And, he, answering, said—He that soweth the good seed, is the Son of Man;
38 Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne’ya’yan mugun nan,
And, the field, is the world, and, the good seed, these are the sons of the kingdom, —and, the darnel seeds, are the sons of the evil one;
39 abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn g165)
And, the enemy that sowed them, is the adversary, and, the harvest, is, the conclusion of an age, and, the reapers, are, messengers. (aiōn g165)
40 “Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn g165)
Just, therefore, as collected is the darnel, and, with fire is burned, so, will it be in the conclusion of the age: — (aiōn g165)
41 Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
The Son of Man will send forth his messengers, and they will collect, out of his kingdom, all the causes of stumbling, and the doers of lawlessness,
42 Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
and will cast them into the furnace of fire: there, will be wailing and gnashing of teeth.
43 Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Then, the righteous, will shine forth as the sun, in the kingdom of their Father. He that hath ears, let him hear!
44 “Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
The kingdom of the heavens is like unto, a treasure hid in the field, which a man, finding, hid, —and, by reason of his joy, withdraweth and selleth whatsoever he hath, and buyeth that field.
45 “Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau.
Again, the kingdom of the heavens is, like, unto, a merchant, seeking beautiful pearls, —
46 Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
and, finding one very precious pearl, departing, he at once sold all things, whatsoever he had, and bought it.
47 “Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri.
Again, the kingdom of the heavens is like unto, a large drag-net, cast into the sea and gathering of every kind, —
48 Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau.
which, when it was filled, they dragged up on the beach, and, sitting down, collected the good into vessels, but, the worthless, forth they cast.
49 Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn g165)
So, will it be in the conclusion of the age: The messengers will come forth, and separate the wicked from among the righteous; (aiōn g165)
50 su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
and will cast them into the furnace of fire: there, will be wailing and gnashing of teeth.
51 Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?” Suka amsa, “I.”
Have ye understood all these things? They say unto him, Yea!
52 Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”
And, he, said unto them—Wherefore, every scribe, discipled unto the kingdom of the heavens, is like unto a householder, who putteth forth out of his treasure, things new and old.
53 Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can.
And it came to pass, when Jesus had finished these parables, he removed from thence;
54 Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka?
and, coming into his own city, began teaching them in their synagogue, so that with astonishment were they being struck, and were saying—Whence, hath, this one, this wisdom, and the mighty works?
55 Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu,’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba?
Is not, this one, the carpenter’s, son? Is not, his mother, called Mary, and are not his brethren—James and Joseph, and Simon, and Judas?
56 Duk’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?”
and, his sisters, are they not all with us? Whence, then hath, this one, all these things?
57 Sai suka ji haushinsa. Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”
And they began to find cause of stumbling in him. But, Jesus, said unto them—A prophet is not without honour, save in his city, and in his house.
58 Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.
And he did not, there, many mighty works, because of their unbelief.

< Mattiyu 13 >