< Mattiyu 13 >

1 A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin.
And in that day Jesus, having gone forth from the house, was sitting by the sea,
2 Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci.
and gathered together to Him were many multitudes, so that He having gone into the boat sat down, and all the multitude on the beach stood,
3 Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
and He spoke to them many things in allegories, saying, “Behold, the sower went forth to sow,
4 Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su.
and in his sowing, some indeed fell by the way, and the birds having come, devoured them,
5 Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi.
and others fell on the rocky places where they did not have much earth, and immediately they sprang forth, through having no depth of earth,
6 Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai.
and the sun having risen they were scorched, and through having no root, they withered,
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su.
and others fell on the thorns, and the thorns came up and choked them,
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka.
and others fell on the good ground, and were giving fruit, some indeed a hundredfold, and some sixty, and some thirty.
9 Duk mai kunnen ji, yă ji.”
He who is having ears to hear—let him hear.”
10 Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”
And the disciples having come near, said to Him, “Why do You speak to them in allegories?”
11 Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba.
And He answering said to them that, “To you it has been given to know the secrets of the kingdom of the heavens, and to these it has not been given,
12 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe.
for whoever has, it will be given to him, and he will have overabundance, and whoever has not, even that which he has will be taken from him.
13 Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan. “Ko da yake suna kallo, ba sa gani; ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.
Because of this, in allegories I speak to them, because seeing they do not see, and hearing they do not hear, nor understand,
14 A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, “‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba; za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
and fulfilled on them is the prophecy of Isaiah that says, With hearing you will hear, and you will not understand, and seeing you will see, and you will not perceive,
15 Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
for the heart of this people was made obtuse, and with the ears they barely heard, and they closed their eyes, lest they might see with the eyes, and might hear with the ears, and understand with the heart, and turn back, and I might heal them.
16 Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji.
And blessed are your eyes because they see, and your ears because they hear,
17 Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.
for truly I say to you that many prophets and righteous men desired to see that which you look on, and they did not see, and to hear that which you hear, and they did not hear.
18 “To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan.
You, therefore, hear the allegory of the sower:
19 Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya.
Everyone hearing the word of the kingdom, and not understanding—the evil one comes, and snatches that which has been sown in his heart; this is that sown by the way.
20 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna.
And that sown on the rocky places, this is he who is hearing the word, and immediately with joy is receiving it,
21 Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya.
and he has no root in himself, but is temporary, and persecution or tribulation having happened because of the word, immediately he is stumbled.
22 Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn g165)
And that sown toward the thorns, this is he who is hearing the word, and the anxiety of this age, and the deceitfulness of the riches, chokes the word, and it becomes unfruitful. (aiōn g165)
23 Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”
And that sown on the good ground: this is he who is hearing the word, and is understanding, who indeed bears fruit, and makes, some indeed a hundredfold, and some sixty, and some thirty.”
24 Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa.
Another allegory He set before them, saying, “The kingdom of the heavens was likened to a man sowing good seed in his field,
25 Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa.
and while men are sleeping, his enemy came and sowed darnel in the midst of the wheat, and went away,
26 Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.
and when the herb sprang up, and yielded fruit, then appeared also the darnel.
27 “Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’
And the servants of the householder, having come near, said to him, Lord, did you not sow good seed in your field? From where then does it have the darnel?
28 “Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’ “Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’
And he says to them, A man, an enemy, did this; and the servants said to him, Will you, then, [that] having gone away we may gather it up?
29 “Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar.
And he said, No, lest—gathering up the darnel—you root up with it the wheat;
30 Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’”
permit both to grow together until the harvest, and in the time of the harvest I will say to the reapers, Gather up first the darnel, and bind it in bundles, to burn it, and the wheat gather up into my storehouse.”
31 Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa.
Another allegory He set before them, saying, “The kingdom of the heavens is like to a grain of mustard, which a man having taken, sowed in his field,
32 Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”
which less, indeed, is than all the seeds, but when it may be grown, is greatest of the herbs, and becomes a tree, so that the birds of the sky come and rest in its branches.”
33 Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”
Another allegory He spoke to them: “The kingdom of the heavens is like to leaven, which a woman having taken, hid in three measures of meal, until the whole was leavened.”
34 Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai.
All these things Jesus spoke in allegories to the multitudes, and without an allegory He was not speaking to them,
35 Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa, “Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”
that it might be fulfilled that was spoken through the prophet, saying, “I will open in allegories My mouth, I will utter things having been hidden from the foundation of the world.”
36 Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”
Then having let away the multitudes, Jesus came into the house, and His disciples came near to Him, saying, “Explain to us the allegory of the darnel of the field.”
37 Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum.
And He answering said to them, “He who is sowing the good seed is the Son of Man,
38 Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne’ya’yan mugun nan,
and the field is the world, and the good seed, these are the sons of the kingdom, and the darnel are the sons of the evil one,
39 abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn g165)
and the enemy who sowed them is the Devil, and the harvest is [the] full end of the age, and the reapers are messengers. (aiōn g165)
40 “Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn g165)
As, then, the darnel is gathered up, and is burned with fire, so will it be in the full end of this age; (aiōn g165)
41 Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
the Son of Man will send forth His messengers, and they will gather up out of His kingdom all the stumbling-blocks, and those doing the lawlessness,
42 Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
and will cast them into the furnace of the fire; there will be the weeping and the gnashing of the teeth.
43 Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Then will the righteous shine forth as the sun in the kingdom of their Father. He who is having ears to hear—let him hear.
44 “Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
Again, the kingdom of the heavens is like to treasure hid in the field, which a man having found, hid, and from his joy goes, and all, as much as he has, he sells, and buys that field.
45 “Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau.
Again, the kingdom of the heavens is like to a man, a merchant, seeking good pearls,
46 Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
who having found one pearl of great price, having gone away, has sold all, as much as he had, and bought it.
47 “Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri.
Again, the kingdom of the heavens is like to a net that was cast into the sea, and gathered together of every kind,
48 Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau.
which, when it was filled, having drawn up again on the beach, and having sat down, they gathered the good into vessels, and the bad they cast out,
49 Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn g165)
so will it be in the full end of the age, the messengers will come forth and separate the evil out of the midst of the righteous, (aiōn g165)
50 su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
and will cast them into the furnace of the fire; there will be the weeping and the gnashing of the teeth.”
51 Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?” Suka amsa, “I.”
Jesus says to them, “Did you understand all these?” They say to Him, “Yes, Lord.”
52 Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”
And He said to them, “Because of this, every scribe having been discipled in regard to the kingdom of the heavens is like to a man, a householder, who brings forth out of his treasure things new and old.”
53 Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can.
And it came to pass, when Jesus finished these allegories, He removed from there,
54 Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka?
and having come to His own country, He was teaching them in their synagogue, so that they were astonished, and were saying, “From where to this One this wisdom and the mighty works?
55 Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu,’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba?
Is this not the carpenter’s Son? Is His mother not called Mary, and His brothers James, and Joses, and Simon, and Judas?
56 Duk’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?”
And His sisters—are they not all with us? From where, then, to this One all these?”
57 Sai suka ji haushinsa. Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”
And they were stumbled at Him. And Jesus said to them, “A prophet is not without honor except in his own country, and in his own house”:
58 Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.
and He did not do many mighty works there, because of their unbelief.

< Mattiyu 13 >