< Mattiyu 12 >
1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
V tem času je šel Jezus v soboto skozi setve; učenci njegovi pa postanejo lačni, in začnó klasje trgati in jesti.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
Ko pa Farizeji to vidijo, rekó mu: "Glej, učenci tvoji delajo, kar se v soboto ne sme delati.
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
On jim pa reče: Niste li brali, kaj je storil David, ko se je ulakotil on in kteri so bili ž njim?
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
Kako je šel v hišo Božjo in je snedel postavljene kruhe, kterih ni smel nihče jesti, razen edini duhovni?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Ali niste li brali v postavi, da skrunijo v soboto duhovni v tempeljnu soboto, in niso krivi?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
Pravim vam pa, da je tu veči od tempeljna.
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
Ko bi pa vedeli, kaj se pravi: "Milosti hočem, in ne darú," ne bi obsojevali nedolžnih.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
Kajti sin človečji je gospodar tudi sobote.
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
In odide odtod, in pride v njih shajališče.
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
In glej, bil je tu človek, kteri je imel suho roko. In vprašajo ga, govoreč: Ali se sme v soboto zdraviti? da bi ga zatožili.
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
On jim pa reče: Kdo med vami je človek, kteri ima eno ovco, in če mu ta pade v soboto v jamo, da je ne bo zgrabil in izvlekel?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
In koliko bolji je človek od ovce? Zatorej se sme v soboto dobro delati.
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Tedaj reče človeku: Stegni roko svojo! Pa stegne, in zdrava je bila kakor druga.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
Farizeji pa izidejo in se posvetujejo za-nj, kako bi ga pogubili.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
Jezus pa zvé, in odide odtod. In za njim je šlo mnogo ljudstva, in uzdravi jih vse.
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
In zapretí jim, naj ga ne razglasé,
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
Da se izpolni, kar je rečeno po preroku Izaiji, kteri pravi:
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
"Glej, hlapec moj, ki sem ga izvolil; ljubljeni moj, ki je duši mojej po volji: duh svoj bom položil na-nj, in oznanjeval bo sodbo narodom.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
Ne bo se prepiral, ne vpil; in nikdor ne bo slišal glasú njegovega po ulicah.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
Nalomljenega trsta ne bo prelomil, in vnetega lanú ne bo pogasil, dokler ne pridobí sodbi zmage.
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
In v ime njegovo bodo zaupali narodi."
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Tedaj mu pripeljejo obsedenca, kteri je bil slep in mutast. In uzdravi ga, da je slepec in mutec govoril in videl.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
In vse ljudstvo se je zavzemalo, govoreč: Ali ni ta sin Davidov?
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
Slišavši pa to Farizeji, rekó: Ta ne izganja hudičev, razen z Belzebulom poglavarjem hudičev.
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
Jezus je pa vedel njih misli, in reče jim: Vsako kraljestvo, ktero se je samo zoper sebe razdvojilo, opustelo bo; in vsako mesto ali dom, kteri se je sam zoper sebe razdvojil, ne bo obstal.
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
In če satan izganja satana, razdvojil se je sam zoper sebe: kako bo terej obstalo kraljestvo njegovo?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
In če jaz z Belzebulom izganjam hudiče, s čegavo pomočjo izganjajo sinovi vaši? Za to vam bodo oni sodniki.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
Če pa jaz s pomočjo Duha Božjega izganjam hudiče, prišlo je torej k vam kraljestvo Božje.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Ali kako more kdo močnemu priti v hišo in mu pohištvo pobrati, če močnega poprej ne zveže? in tedaj bo okradel hišo njegovo.
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
Kdor ni z menoj, proti meni je; in kdor z menoj ne zbira, razsiplje.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Za to vam pravim: Vsak greh in vsaka kletvina se bo odpustila ljudém; kletvina zoper Duhá se pa ne bo odpustila ljudém.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn )
In če reče kdo besedo zoper sina človečjega, odpustilo mu se bo; kdor pa reče zoper svetega Duha, ne bo mu se odpustilo, ne v tem veku ne v prihodnjem. (aiōn )
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
Ali vsadite dobro drevo, in sad njegov bo dober; ali vsadite slabo drevo, in sad njegov bo slab: kajti drevo se pozná po sadu.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
Gadja zalega! kako morete dobro govoriti, ko ste hudobni? kajti usta govoré od preobilnosti srca.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
Dober človek prinaša iz dobrega zaklada srca dobro; in hudoben človek prinaša iz hudobnega zaklada hudobno.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
Pravim vam pa, da za vsako prazno besedo, kterokoli rekó ljudjé, dali bodo za njo odgovor v dan sodbe.
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
Kajti s svojimi besedami se boš opravičil, in s svojimi besedami se boš obsodil.
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Tedaj mu odgovoré nekteri od pismarjev in Farizejev in rekó: Učenik! znamenje hočemo od tebe videti.
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
On pa odgovorí in jim reče: Hudobni in prešestni rod išče znamenja; ali ne bo mu se dalo znamenje, razen znamenje preroka Jonata.
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
Kakor je bil namreč Jona v kitovem trebuhu tri dní in tri nočí, tako bo sin človečji v srcu zemlje tri dní in tri nočí.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
Možjé Ninivljani bodo vstali na sodbo s tem rodom, in obsodili ga bodo; kajti spokorili so se po pridigi Jonata; in glej, tu je veči od Jonata.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
Južna kraljica bo vstala na sodbo s tem rodom, in obsodila ga bo; kajti prišla je od kraja sveta, da sliši Solomonovo modrost; in glej, tu je veči od Solomona.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
Izšedši pa duh nečisti iz človeka, hodi po suhih krajih, in išče pokoja; in ne najde ga.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Tedaj reče: Vrnil se bom v dom svoj, odkoder sem izšel. Ter pride, in najde praznega, očejenega in olepšanega.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Tedaj odide in vzeme s seboj sedem drugih duhov, hujih od sebe, ter vnidejo, in tu prebivajo: in poslednje bo temu človeku huje od prvega. Tako bo tudi temu hudobnemu rodu.
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
Ko je pa še ljudstvu govoril, glej, mati njegova in bratje njegovi so stali zunaj, in radi bi bili ž njim govorili.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
In nekdo mu reče: Glej, mati tvoja in bratje tvoji stojé zunaj, in radi bi s teboj govorili.
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
On pa odgovorí, in reče tistemu, ki mu je povedal: Kdo je mati moja? in kdo so bratje moji?
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
In stegnivši roko svojo na učence svoje, reče: Glej, mati moja in bratje moji!
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
Kajti kdorkoli izpolni voljo očeta mojega, ki je na nebesih, on je brat moj in sestra in mati.