< Mattiyu 12 >

1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
Ob tistem času je šel Jezus na šabatni dan skozi žitna polja, njegovi učenci pa so bili lačni in začeli smukati žitno klasje ter jesti.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
Toda ko so to videli farizeji, so mu rekli: »Glej, tvoji učenci delajo to, česar ni zakonito početi na šabatni dan.«
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
Toda rekel jim je: »Ali niste brali, kaj je storil David, ko je bil lačen in tisti, ki so bili z njim,
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
kako je vstopil v Božjo hišo in jedel hlebe navzočnosti, ki jih ni bilo dovoljeno jesti njemu niti ne tistim, ki so bili z njim, temveč samo duhovnikom?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Ali niste brali v postavi, kako to, da ob šabatnih dneh duhovniki v templju skrunijo šabat in so brez krivde?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
Toda povem vam: ›Da je na tem kraju nekdo večji kakor tempelj.‹
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
Toda če bi vedeli, kaj to pomeni: ›Usmiljenje hočem imeti in ne žrtve, ‹ ne bi obsojali nedolžnih.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
Kajti Sin človekov je Gospod celó šabatnemu dnevu.«
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
In ko je odšel od tam, je šel v njihovo sinagogo.
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
In glej, tam je bil človek, ki je imel svojo roko izsušeno. In da bi ga lahko obdolžili, so ga vprašali, rekoč: »Ali je zakonito zdraviti na šabatne dneve?«
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
In rekel jim je: »Kateri človek bi bil tukaj med vami, ki bi imel eno ovco in če bi ta na šabatni dan padla v jamo ali je ne bi prijel ter je dvignil ven?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
Koliko bolj je potem človek boljši kakor ovca? Zaradi tega je na šabatne dneve zakonito delati dobro.«
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Tedaj reče človeku: »Iztegni svojo roko.« In ta jo je iztegnil in bila je v celoti ozdravljena, podobno kakor druga.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
Potem so farizeji odšli ven in imeli zborovanje proti njemu, kako bi ga lahko pokončali.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
Toda ko je Jezus to izvedel, se je umaknil od tam in sledile so mu velike množice in vse je ozdravil
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
ter jim naročil, da naj ga ne razglašajo,
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
da bi se lahko izpolnilo, kar je bilo rečeno po preroku Izaiju, rekoč:
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
›Glej moj služabnik, ki sem ga izbral, moj ljubljeni, v katerem je moja duša zelo zadovoljna. Svojega duha bom položil nadenj in oznanil bo sodbo poganom.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
Ne bo se ne prepiral niti ne vpil niti na ulicah nihče ne bo slišal njegovega glasu.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
Poškodovanega trsta ne bo zlomil in kadečega stenja ne bo pogasil, dokler ne privede sodbe do zmage.
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
In v njegovo ime bodo zaupali pogani.‹
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Tedaj je bil k njemu priveden nekdo obseden s hudičem, slep in nem in ga je ozdravil, do take mere, da je slepi in nemi tako govoril kakor videl.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
In vsa množica je bila osupla ter rekla: »Ali ni ta Davidov sin?«
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
Toda ko so farizeji to slišali, so rekli: »Ta ne izganja hudičev, razen z Bélcebubom, princem hudičev.«
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
Jezus pa je poznal njihove misli in jim rekel: »Vsako kraljestvo, razdeljeno zoper sebe, je privedeno v opustošenje in nobeno mesto ali hiša, razdeljena zoper sebe, ne bosta obstala.
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
In če Satan izganja Satana, je razdeljen zoper sebe; kako bo potem obstalo njegovo kraljestvo?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
In če z Bélcebubom izganjam hudiče, s kom jih izganjajo vaši otroci? Zatorej bodo oni vaši sodniki.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
Toda če z Božjim Duhom izganjam hudiče, potem je k vam prišlo Božje kraljestvo.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Kako lahko sicer nekdo vstopi v hišo močnega in opleni njegove dobrine, razen če najprej ne zveže močnega? In tedaj bo oplenil njegovo hišo.
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
Kdor ni z menoj, je proti meni; in kdor ne zbira z menoj, razsipa na široko.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Zatorej vam pravim: ›Vsake vrste greh in bogokletje bo ljudem odpuščeno, toda bogokletje zoper Svetega Duha ljudem ne bo odpuščeno.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn g165)
In kdorkoli govori besedo zoper Sina človekovega, mu bo to odpuščeno; toda kdorkoli govori zoper Svetega Duha, mu ne bo odpuščeno ne na tem svetu ne v svetu, ki pride.‹ (aiōn g165)
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
Ali drevo dobro obrodi in je njegov sad dober, ali pa drevo slabo obrodi in je njegov sad slab; kajti drevo se spozna po njegovem sadu.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
Oh gadji rod, kako lahko vi, ki ste hudobni, govorite dobre besede? Kajti iz obilja srca usta govoré.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
Dober človek iz dobrega zaklada srca prinaša dobre stvari, hudobnež pa iz zlega zaklada prinaša zle stvari.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
Toda povem vam: ›Za vsako prazno besedo, ki jo bodo ljudje izgovorili, bodo na dan sodbe o tem dajali obračun.‹
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
Kajti po svojih besedah boš opravičen in po svojih besedah boš obsojen.«
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Tedaj so nekateri izmed pisarjev in farizejev odgovorili, rekoč: »Učitelj, od tebe želimo videti znamenje.«
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
Toda odgovoril jim je in rekel: »Hudoben in zakonolomen rod išče znamenje, pa mu ne bo dano nobeno drugo znamenje, razen znamenja preroka Jona.
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
Kajti tako, kakor je bil Jona tri dni in tri noči v kitovem trebuhu, tako bo Sin človekov tri dni in tri noči v osrčju zemlje.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
Ljudje iz Niniv bodo ob sodbi vstali s tem rodom in ga obsodili, ker so se ob Jonovem oznanjevanju pokesali; in glejte, tukaj je večji kakor Jona.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
Kraljica z juga bo ob sodbi vstala s tem rodom in ga obsodila, kajti prišla je iz najbolj oddaljenih krajev zemlje, da sliši Salomonovo modrost; in glejte, tukaj je večji kakor Salomon.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
Kadar je nečisti duh odšel iz človeka, hodi po suhih krajih, iščoč počitka, in ga ne najde.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Potem reče: ›Vrnil se bom v svojo hišo, od koder sem izšel.‹ In ko pride, jo najde prazno, pometeno in okrašeno.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Tedaj gre in s seboj vzame sedem drugih duhov, zlobnejših kakor on sam in vstopijo ter prebivajo tam in končno stanje tega človeka je slabše kakor prvo. Točno tako bo tudi temu zlobnemu rodu.«
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
Medtem ko je še govoril množici, glej, so stali zunaj njegova mati in njegovi bratje, želeč govoriti z njim.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
Potem mu je nekdo rekel: »Glej, tvoja mati in tvoji bratje stojijo zunaj in želijo govoriti s teboj.«
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
Toda odgovoril je in rekel tistemu, ki mu je povedal: »Kdo je moja mati? In kdo so moji bratje?«
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
In svojo roko je iztegnil proti svojim učencem ter rekel: »Glejte, moja mati in moji bratje!
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
Kajti kdorkoli bo izvrševal voljo mojega Očeta, ki je v nebesih, ta je moj brat in sestra in mati.«

< Mattiyu 12 >