< Mattiyu 12 >
1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
In that tyme Jhesus wente bi cornes in the sabot day; and hise disciplis hungriden, and bigunnen to plucke the eris of corn, and to ete.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
And Fariseis, seynge, seiden to hym, Lo! thi disciplis don that thing that is not leueful to hem to do in sabatis.
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
And he seide to hem, Whether ye han not red, what Dauid dide, whanne he hungride, and thei that weren with hym?
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
hou he entride in to the hous of God, and eet looues of proposicioun, whiche looues it was not leueful to hym to ete, nether to hem that weren with hym, but to prestis aloone?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Or whether ye han not red in the lawe, that in sabotis prestis in the temple defoulen the sabotis, and thei ben with oute blame?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
And Y seie to you, that here is a gretter than the temple.
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
And if ye wisten, what it is, Y wole merci, and not sacrifice, ye schulden neuer haue condempned innocentis.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
For mannus Sone is lord, yhe, of the sabat.
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
And whanne he passide fro thennus, he cam in to the synagoge of hem.
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
And lo! a man that hadde a drye hoond. And thei axiden hym, and seiden, Whether it be leueful to hele in the sabot? that thei schulden acuse hym.
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
And he seide to hem, What man of you schal be, that hath o scheep, and if it falle in to a diche in the sabotis, whether he shal not holde, and lifte it vp?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
How myche more is a man better than a scheep? Therfor it is leueful to do good in the sabatis.
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Thanne he seide to the man, Stretche forth thin hoond. And he strauyte forth; and it was restorid to heelthe as the tothir.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
And the Farisees wenten out, and maden a counsel ayens hym, hou thei schulden distrie hym.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
And Jhesus knewe it, and wente awei fro thennus; and many sueden hym, and he helide hem alle.
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
And he comaundide to hem, that thei schulden not make hym knowun;
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
that that thing were fulfillid, that was seid by Isaie, the prophete, seiynge, Lo!
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
my child, whom Y haue chosun, my derling, in whom it hath wel plesid to my soule; Y shal put my spirit on him, and he shal telle dom to hethen men.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
He shal not stryue, ne crye, nethir ony man shal here his voice in stretis.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
A brisid rehed he shal not breke, and he schal not quenche smokynge flax, til he caste out doom to victorie;
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
and hethene men schulen hope in his name.
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Thanne a man blynde and doumbe, that hadde a feend, was brouyt to hym; and he helide hym, so that he spak, and say.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
And al the puple wondride, and seide, Whether this be the sone of Dauid?
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
But the Farisees herden, and seiden, He this casteth not out feendis, but in Belsabub, prince of feendis.
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
And Jhesus, witynge her thouytis, seide to hem, Eche kingdom departid ayens it silf, schal be desolatid, and eche cite, or hous, departid ayens it self, schal not stonde.
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
And if Satanas castith out Satanas, he is departid ayens him silf; therfor hou schal his kingdom stonde?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
And if Y in Belsabub caste out deuelis, in `whom youre sones casten out? Therfor thei schulen be youre domes men.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
But if Y in the Spirit of God caste out feendis, thanne the kyngdom of God is comen in to you.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Ethir hou may ony man entre in to the hous of a stronge man, and take awey hise vesselis, but `he first bynde the stronge man, and thanne he schal spuyle his hous?
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
He that is not with me, is ayens me; and he that gaderith not togidere with me, scaterith abrood.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Therfor I seie to you, al synne and blasfemye shal be foryouun to men, but `the spirit of blasfemye shal not be foryouun.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn )
And who euere seith a word ayens mannus sone, it shal be foryouun to him; but who that seieth a word ayens the Hooli Goost, it shal not be foryouun to hym, nether in this world, ne in `the tothir. (aiōn )
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
Ethir make ye the tree good, and his fruyt good; ether make ye the tree yuel and his fruyt yuel; for a tree is knowun of the fruyt.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
Ye generacioun of eddris, hou moun ye speke goode thingis, whanne ye ben yuele? For the mouth spekith of plente of the herte.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
A good man bryngith forth good thingis of good tresoure, and an yuel man bringith forth yuel thingis of yuel tresoure.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
And Y seie to you, that of euery idel word, that men speken, thei schulen yelde resoun therof in the dai of doom;
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
for of thi wordis thou schalt be iustified, and of thi wordis thou shalt be dampned.
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Thanne summe of the scribis and Farisees answeriden to hym, and seiden, Mayster, we wolen se a tokne of thee.
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
Which answeride, and seide to hem, An yuel kynrede and a spouse brekere sekith a tokene, and a tokene shal not be youun to it, but the tokene of Jonas, the prophete.
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
For as Jonas was in the wombe of a whal thre daies and thre nyytis, so mannus sone shal be in the herte of the erthe thre daies and thre nyytis.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
Men of Nynyue schulen rise in doom with this generacioun, and schulen condempne it; for thei diden penaunce in the prechyng of Jonas, and lo! here a gretter than Jonas.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
The queene of the south shal rise in doom with this generacioun, and schal condempne it; for she cam fro the eendis of the erthe to here the wisdom of Salomon, and lo! here a gretter than Salomon.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
Whanne an vnclene spirit goith out fro a man, he goith bi drie places, `and sekith rest, and fyndith not.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Thanne he seith, Y shal turne ayen in to myn hous, fro whannys Y wente out. And he cometh, and fyndith it voide, and clensid with besyms, and maad faire.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Thanne he goith, and takith with him seuene othere spiritis worse than hym silf; and thei entren, and dwellen there. And the laste thingis of that man ben maad worse than the formere. So it shal be to this worste generacioun.
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
Yit whil he spak to the puple, lo! his modir and his bretheren stoden withouteforth, sekynge to speke to hym.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
And a man seide to hym, Lo! thi modir and thi britheren stonden withouteforth, sekynge thee.
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
He answeride to the man, that spak to hym, and seide, Who is my modir? and who ben my britheren?
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
And he helde forth his hoond in to hise disciplis, and seide, Lo! my modir and my bretheren;
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
for who euer doith the wille of my fadir that is in heuenes, he is my brothir, and sistir, and modir.