< Mattiyu 12 >
1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
At that time, Yeshua went on the Sabbath day through the grain fields. His disciples were hungry and began to pluck heads of grain and to eat.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
But the Pharisees, when they saw it, said to him, “Behold, your disciples do what is not lawful to do on the Sabbath.”
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
But he said to them, “Haven’t you read what David did when he was hungry, and those who were with him:
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
how he entered into God’s house and ate the show bread, which was not lawful for him to eat, nor for those who were with him, but only for the priests?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Or have you not read in the law that on the Sabbath day the priests in the temple profane the Sabbath and are guiltless?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
But I tell you that one greater than the temple is here.
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
But if you had known what this means, ‘I desire mercy, and not sacrifice,’ you wouldn’t have condemned the guiltless.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
For the Son of Man is Lord of the Sabbath.”
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
He departed from there and went into their synagogue.
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
And behold, there was a man with a withered hand. They asked him, “Is it lawful to heal on the Sabbath day?” so that they might accuse him.
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
He said to them, “What man is there amongst you who has one sheep, and if this one falls into a pit on the Sabbath day, won’t he grab on to it and lift it out?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
Of how much more value then is a man than a sheep! Therefore it is lawful to do good on the Sabbath day.”
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Then he told the man, “Stretch out your hand.” He stretched it out; and it was restored whole, just like the other.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
But the Pharisees went out and conspired against him, how they might destroy him.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
Yeshua, perceiving that, withdrew from there. Great multitudes followed him; and he healed them all,
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
and commanded them that they should not make him known,
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
that it might be fulfilled which was spoken through Isaiah the prophet, saying,
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
“Behold, my servant whom I have chosen, my beloved in whom my soul is well pleased. I will put my Spirit on him. He will proclaim justice to the nations.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
He will not strive, nor shout, neither will anyone hear his voice in the streets.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
He won’t break a bruised reed. He won’t quench a smoking flax, until he leads justice to victory.
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
In his name, the nations will hope.”
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Then one possessed by a demon, blind and mute, was brought to him; and he healed him, so that the blind and mute man both spoke and saw.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
All the multitudes were amazed, and said, “Can this be the son of David?”
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
But when the Pharisees heard it, they said, “This man does not cast out demons except by Beelzebul, the prince of the demons.”
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
Knowing their thoughts, Yeshua said to them, “Every kingdom divided against itself is brought to desolation, and every city or house divided against itself will not stand.
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
If Satan casts out Satan, he is divided against himself. How then will his kingdom stand?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
If I by Beelzebul cast out demons, by whom do your children cast them out? Therefore they will be your judges.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
But if I by the Spirit of God cast out demons, then God’s Kingdom has come upon you.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Or how can one enter into the house of the strong man and plunder his goods, unless he first bind the strong man? Then he will plunder his house.
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
“He who is not with me is against me, and he who doesn’t gather with me, scatters.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Therefore I tell you, every sin and blasphemy will be forgiven men, but the blasphemy against the Spirit will not be forgiven men.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn )
Whoever speaks a word against the Son of Man, it will be forgiven him; but whoever speaks against the Holy Spirit, it will not be forgiven him, either in this age, or in that which is to come. (aiōn )
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
“Either make the tree good and its fruit good, or make the tree corrupt and its fruit corrupt; for the tree is known by its fruit.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
You offspring of vipers, how can you, being evil, speak good things? For out of the abundance of the heart, the mouth speaks.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
The good man out of his good treasure brings out good things, and the evil man out of his evil treasure brings out evil things.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
I tell you that every idle word that men speak, they will give account of it in the day of judgement.
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
For by your words you will be justified, and by your words you will be condemned.”
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Then certain of the scribes and Pharisees answered, “Rabbi, we want to see a sign from you.”
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
But he answered them, “An evil and adulterous generation seeks after a sign, but no sign will be given to it but the sign of Jonah the prophet.
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
For as Jonah was three days and three nights in the belly of the huge fish, so will the Son of Man be three days and three nights in the heart of the earth.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
The men of Nineveh will stand up in the judgement with this generation and will condemn it, for they repented at the proclaiming of Jonah; and behold, someone greater than Jonah is here.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
The Queen of the South will rise up in the judgement with this generation and will condemn it, for she came from the ends of the earth to hear the wisdom of Solomon; and behold, someone greater than Solomon is here.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
“When an unclean spirit has gone out of a man, he passes through waterless places seeking rest, and doesn’t find it.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Then he says, ‘I will return into my house from which I came;’ and when he has come back, he finds it empty, swept, and put in order.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Then he goes and takes with himself seven other spirits more evil than he is, and they enter in and dwell there. The last state of that man becomes worse than the first. Even so will it be also to this evil generation.”
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
While he was yet speaking to the multitudes, behold, his mother and his brothers stood outside, seeking to speak to him.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
One said to him, “Behold, your mother and your brothers stand outside, seeking to speak to you.”
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
But he answered him who spoke to him, “Who is my mother? Who are my brothers?”
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
He stretched out his hand towards his disciples, and said, “Behold, my mother and my brothers!
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
For whoever does the will of my Father who is in heaven, he is my brother, and sister, and mother.”