< Mattiyu 12 >
1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
At that time Jesus went on the sabbath through the grain fields; and his disciples were hungry, and began to pluck the heads of grain, and to eat.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
But when the Pharisees saw it, they said to him, Behold, thy disciples do that which it is not lawful to do on the sabbath.
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
But he said to them, Have ye not read what David did, when he was hungry, and they that were with him;
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
How he entered into the house of God, and ate the showbread, which it was not lawful for him to eat, neither for them who were with him, but only for the priests?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Or have ye not read in the law, that on the sabbath the priests in the temple profane the sabbath, and are blameless?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
But I say to you, That in this place is one greater than the temple.
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
But if ye had known what this meaneth, I will have mercy, and not sacrifice, ye would not have condemned the guiltless.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
For the Son of man is Lord even of the sabbath.
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
And when he had departed from there, he went into their synagogue:
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
And, behold, there was a man who had his hand withered. And they asked him, saying, Is it lawful to heal on the sabbath? that they might accuse him.
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
And he said to them, What man shall there be among you, that shall have one sheep, and if it shall fall into a pit on the sabbath, will he not lay hold on it, and lift it out?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
How much then is a man better than a sheep? Therefore it is lawful to do good on the sabbath days.
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Then saith he to the man, Stretch out thy hand. And he stretched it out; and it was restored as whole, as the other.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
Then the Pharisees went out, and held a council against him, how they might destroy him.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
But when Jesus knew it, he withdrew himself from there: and great multitudes followed him, and he healed them all;
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
And charged them that they should not make him known:
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
That it might be fulfilled which was spoken by Isaiah the prophet, saying,
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
Behold my servant, whom I have chosen; my beloved, in whom my soul is well pleased: I will put my spirit upon him, and he shall show justice to the Gentiles.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
He shall not quarrel, nor cry; neither shall any man hear his voice in the streets.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
A bruised reed shall he not break, and smoking flax shall he not quench, till he shall send forth justice to victory.
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
And in his name shall the Gentiles trust.
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Then was brought to him one possessed with a demon, blind, and dumb: and he healed him, so that the blind and dumb both spoke and saw.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
And all the people were amazed, and said, Is not this the son of David?
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
But when the Pharisees heard it, they said, This man doth not cast out demons, but by Beelzebub the prince of the demons.
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
And Jesus knew their thoughts, and said to them, Every kingdom divided against itself is brought to desolation; and every city or house divided against itself shall not stand:
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
And if Satan casteth out Satan, he is divided against himself; how then shall his kingdom stand?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
And if I by Beelzebub cast out demons, by whom do your children cast them out? therefore they shall be your judges.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
But if I cast out demons by the Spirit of God, then the kingdom of God is come to you.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Or else how can one enter into a strong man’s house, and seize his goods, except he shall first bind the strong man? and then he will plunder his house.
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
He that is not with me is against me; and he that gathereth not with me scattereth abroad.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Therefore I say to you, All manner of sin and blasphemy shall be forgiven to men: but the blasphemy against the Holy Spirit shall not be forgiven to men.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn )
And whoever speaketh a word against the Son of man, it shall be forgiven him: but whoever speaketh against the Holy Spirit, it shall not be forgiven him, neither in this world, neither in the world to come. (aiōn )
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
Either make the tree good, and its fruit good; or else make the tree corrupt, and its fruit corrupt: for the tree is known by its fruit.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
O generation of vipers, how can ye, being evil, speak good things? for out of the abundance of the heart the mouth speaketh.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
A good man out of the good treasure of the heart bringeth forth good things: and an evil man out of the evil treasure bringeth forth evil things.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
But I say to you, That for every idle word that men shall speak, they shall give account for it in the day of judgment.
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
For by thy words thou shalt be justified, and by thy words thou shalt be condemned.
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Then certain of the scribes and of the Pharisees answered, saying, Master, we would see a sign from thee.
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
But he answered and said to them, An evil and adulterous generation seeketh for a sign; and there shall no sign be given to it, but the sign of the prophet Jonah:
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
For as Jonah was three days and three nights in the belly of the great fish so shall the Son of man be three days and three nights in the heart of the earth.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
The men of Nineveh shall rise in judgment with this generation, and shall condemn it: because they repented at the preaching of Jonah; and, behold, a greater than Jonah is here.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
The queen of the south shall rise up in the judgment with this generation, and shall condemn it: for she came from the ends of the earth to hear the wisdom of Solomon; and, behold, a greater than Solomon is here.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
When the unclean spirit is gone out of a man, he walketh through dry places, seeking rest, and he findeth none.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Then he saith, I will return into my house from which I came out; and when he is come, he findeth it empty, swept, and garnished.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Then goeth he, and taketh with himself seven other spirits more wicked than himself, and they enter in and dwell there: and the last state of that man is worse than the first. Even so shall it be also to this wicked generation.
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
While he was yet speaking to the people, behold, his mother and his brethren stood outside, desiring to speak with him.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
Then one said to him, Behold, thy mother and thy brethren stand outside, desiring to speak with thee.
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
But he answered and said to him that told him, Who is my mother? and who are my brethren?
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
And he stretched forth his hand toward his disciples, and said, Behold my mother and my brethren!
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
For whoever shall do the will of my Father who is in heaven, the same is my brother, and sister, and mother.