< Mattiyu 12 >

1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
At that time Iesus went on a Sabbath day through ye corne, and his disciples were an hungred, and bega to plucke ye eares of corne and to eate.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
And when the Pharises sawe it, they saide vnto him, Beholde, thy disciples doe that which is not lawfull to doe vpon the Sabbath.
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
But he said vnto them, Haue ye not read what Dauid did when he was an hungred, and they that were with him?
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
Howe he entred into ye house of God, and did eate the shewe bread, which was not lawfull for him to eate, neither for them which were with him, but onely for the Priestes?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Or haue ye not read in the Lawe, how that on the Sabbath dayes the Priestes in the Temple breake the Sabbath, and are blameles?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
But I say vnto you, that here is one greater then the Temple.
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
Wherefore if ye knewe what this is, I will haue mercie, and not sacrifice, ye would not haue condemned the innocents.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
For the sonne of man is Lord, euen of the Sabbath.
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
And he departed thence, and went into their Synagogue:
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
And beholde, there was a man which had his hand dried vp. And they asked him, saying, Is it lawfull to heale vpon a Sabbath day? that they might accuse him.
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
And he said vnto the, What man shall there be among you, that hath a sheepe, and if it fal on a Sabbath day into a pit, doth not take it and lift it out?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
How much more then is a man better then a sheepe? therefore, it is lawfull to doe well on a Sabbath day.
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Then said he to the man, Stretch forth thine hand. And he stretched it foorth, and it was made whole as the other.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
Then the Pharises went out, and consulted against him, howe they might destroy him.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
But whe Iesus knew it, he departed thece, and great multitudes folowed him, and he healed the al,
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
And charged them in threatning wise, that they should not make him knowen,
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
That it might be fulfilled, which was spoken by Esaias the Prophet, saying,
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
Behold my seruant whom I haue chosen, my beloued in whom my soule deliteth: I wil put my Spirit on him, and he shall shewe iudgement to the Gentiles.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
He shall not striue, nor crie, neither shall any man heare his voyce in the streetes.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
A bruised reede shall he not breake, and smoking flaxe shall he not quenche, till he bring forth iudgement vnto victorie.
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
And in his Name shall the Gentiles trust.
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Then was brought to him one, possessed with a deuill, both blind, and dumme, and he healed him, so that he which was blind and dumme, both spake and saw.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
And all the people were amased, and saide, Is not this that sonne of Dauid?
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
But when the Pharises heard it, they saide, This man casteth the deuils no otherwise out, but through Beelzebub the prince of deuils.
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
But Iesus knew their thoughtes, and said to them, Euery kingdome deuided against it selfe, is brought to nought: and euery citie or house, deuided against it selfe, shall not stand.
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
So if Satan cast out Satan, he is deuided against himself: how shall then his kingdom endure?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
Also if I through Beelzebub cast out deuils, by whom doe your children cast them out? Therefore they shall be your iudges.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
But if I cast out deuils by ye Spirit of God, then is the kingdome of God come vnto you.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Els howe can a man enter into a strong mans house and spoyle his goods, except he first bind the strong man, and then spoile his house.
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
He that is not with me, is against me: and he that gathereth not with me, scattereth.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Wherefore I say vnto you, euery sinne and blasphemie shalbe forgiuen vnto men: but the blasphemie against the holy Ghost shall not be forgiuen vnto men.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn g165)
And whosoeuer shall speake a word against the Sonne of man, it shall be forgiuen him: but whosoeuer shall speake against the holy Ghost, it shall not be forgiuen him, neither in this worlde, nor in the worlde to come. (aiōn g165)
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
Either make the tree good, and his fruite good: or els make the tree euill, and his fruite euil: for the tree is knowen by the fruite.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
O generations of vipers, howe can you speake good things, when ye are euill? For of the abundance of the heart the mouth speaketh.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
A good man out of the good treasure of his heart bringeth foorth good things: and an euill man out of an euill treasure, bringeth forth euill things.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
But I say vnto you, that of euery idle word that men shall speake, they shall giue account thereof at the day of iudgement.
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
For by thy wordes thou shalt be iustified, and by thy wordes thou shalt be condemned.
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Then answered certaine of ye Scribes and of the Pharises, saying, Master, we would see a signe of thee.
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
But he answered and said to them, An euill and adulterous generation seeketh a signe, but no signe shall be giuen vnto it, saue that signe of the Prophet Ionas.
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
For as Ionas was three daies and three nights in the whales belly: so shall the Sonne of man be three daies and three nights in ye heart of the earth.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
The men of Nineue shall rise in iudgement with this generation, and condemne it: for they repented at the preaching of Ionas: and behold, a greater then Ionas is here.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
The Queene of the South shall rise in iudgement with this generation, and shall condemne it: for she came from the vtmost partes of the earth to heare the wisdome of Salomon: and beholde, a greater then Salomon is here.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
Nowe when the vncleane spirit is gone out of a man, he walketh throughout drie places, seeking rest, and findeth none.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Then he saith, I wil returne into mine house from whence I came: and when he is come, he findeth it emptie, swept and garnished.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Then he goeth, and taketh vnto him seuen other spirites worse then himselfe, and they enter in, and dwell there: and the ende of that man is worse then the beginning. Euen so shall it be with this wicked generation.
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
While he yet spake to ye multitude, beholde, his mother, and his brethren stood without, desiring to speake with him.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
Then one said vnto him, Beholde, thy mother and thy brethren stand without, desiring to speake with thee.
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
But he answered, and said to him that told him, Who is my mother? and who are my brethren?
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
And he stretched foorth his hand toward his disciples, and said, Beholde my mother and my brethren.
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
For whosoeuer shall doe my Fathers will which is in heauen, the same is my brother and sister and mother.

< Mattiyu 12 >