< Mattiyu 12 >

1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
På den Tid vandrede Jesus på Sabbaten igennem en Sædemark; men hans Disciple bleve hungrige og begyndte at plukke Aks og at spise.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
Men da Farisæerne så det, sagde de til ham: "Se, dine Disciple gøre, hvad det ikke er tilladt at gøre på en Sabbat."
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
Men han sagde til dem: "Have I ikke læst, hvad David gjorde, da han blev hungrig og de, som vare med ham?
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
hvorledes han gik ind i Guds Hus og spiste Skuebrødene, som det ikke var ham tilladt at spise, ej heller dem, som vare med ham, men alene Præsterne?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Eller have I ikke læst i Loven, at på Sabbaterne vanhellige Præsterne Sabbaten i Helligdommen og ere dog uden Skyld?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
Men jeg siger eder, at her er det, som er større end Helligdommen.
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
Men dersom I havde vidst, hvad det Ord betyder: Jeg har Lyst til Barmhjertighed og ikke til Offer, da havde I ikke fordømt dem, som ere uden Skyld.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
Thi Menneskesønnen er Herre over Sabbaten."
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
Og han gik videre derfra og kom ind i deres Synagoge.
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
Og se, der var en Mand, som havde en vissen Hånd; og de spurgte ham ad og sagde: "Er det tilladt at helbrede på Sabbaten?" for at de kunde anklage ham.
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
Men han sagde til dem: "Hvilket Menneske er der iblandt eder, som har kun eet Får, og ikke tager fat på det og drager det op, dersom det på Sabbaten falder i en Grav?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
Hvor meget er nu ikke et Menneske mere end et Får? Altså er det tilladt at gøre vel på Sabbaten."
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Da siger han til Manden: "Ræk din Hånd ud!" og han rakte den ud, og den blev igen sund som den anden.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
Men Farisæerne gik ud og lagde Råd op imod ham, hvorledes de kunde slå ham ihjel.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
Men da Jesus mærkede det, drog han bort derfra; og mange fulgte ham, og han helbredte dem alle.
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
Og han bød dem strengt, at de ikke måtte gøre ham kendt;
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
for at det skulde opfyldes, som er talt ved Profeten Esajas, som siger:
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
"Se, min Tjener, som jeg har udvalgt, min elskede, i hvem min Sjæl har Velbehag; jeg vil give min Ånd over ham, og han skal forkynde Hedningerne Ret.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
Han skal ikke kives og ikke råbe, og ingen skal høre hans Røst på Gaderne.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
Han skal ikke sønderbryde det knækkede Rør og ikke udslukke den rygende Tande, indtil han får ført Retten frem til Sejr.
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
Og på hans Navn skulle Hedninger håbe."
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Da blev en besat, som var blind og stum, ført til ham; og han helbredte ham, så at den stumme talte og så.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
Og alle Skarerne forfærdedes og sagde: "Mon denne skulde være Davids Søn?"
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
Men da Farisæerne hørte det, sagde de: "Denne uddriver ikke de onde Ånder uden ved Beelzebul, de onde Ånders Fyrste."
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
Men såsom han kendte deres Tanker, sagde han til dem: "Hvert Rige, som er kommet i Splid med sig selv, lægges øde; og hver By eller Hus, som er kommet i Splid med sig selv, kan ikke bestå.
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
Og hvis Satan uddriver Satan, så er han kommen i Splid med sig selv; hvorledes skal da hans Rige bestå?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
Og dersom jeg uddriver de onde Ånder ved Beelzebul, ved hvem uddrive da eders Sønner dem? Derfor skulle de være eders Dommere.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
Men dersom jeg uddriver de onde Ånder ved Guds Ånd, da er jo Guds Rige kommet til eder.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Eller hvorledes kan nogen gå ind i den stærkes Hus og røve hans Ejendele, uden han først binder den stærke? Da kan han plyndre hans Hus.
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
Den, som ikke er med mig, er imod mig; og den, som ikke samler med mig, adspreder.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Derfor siger jeg eder: Al Synd og Bespottelse skal forlades Menneskene, men Bespottelsen imod Ånden skal ikke forlades.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn g165)
Og den, som taler et Ord imod Menneskesønnen, ham skal det forlades; men den som taler imod den Helligånd, ham skal det ikke forlades, hverken i denne Verden eller i den kommende. (aiōn g165)
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
Lader enten Træet være godt og dets Frugt god; eller lader Træet være råddent, og dets Frugt rådden; thi Træet kendes på Frugten.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
I Øgleunger! hvorledes kunne I tale godt, når I ere onde? Thi af Hjertets Overflødighed taler Munden.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
Et godt Menneske fremtager gode Ting af sit gode Forråd; og et ondt Menneske fremtager onde Ting af sit onde Forråd.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
Men jeg siger eder, at Menneskene skulle gøre Regnskab på Dommens Dag for hvert utilbørligt Ord, som de tale.
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
Thi af dine Ord skal du retfærdiggøres, og af dine Ord skal du førdømmes."
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Da svarede nogle af de skriftkloge og Farisæerne ham og sagde: "Mester! vi ønske at se et Tegn at dig."
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
Men han svarede og sagde til dem: "En ond og utro Slægt forlanger Tegn, men der skal intet Tegn gives den uden Profeten Jonas's Tegn.
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
Thi ligesom Jonas var tre Dage og tre Nætter i Havdyrets Bug, således skal Menneskesønnen være tre Dage og tre Nætter i Jordens Skød.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
Mænd fra Ninive skulle opstå ved Dommen sammen med denne Slægt og fordømme den; thi de omvendte sig ved Jonas's Prædiken; og se, her er mere end Jonas.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
Sydens Dronning skal oprejses ved Dommen sammen med denne Slægt og fordømme den; thi hun kom fra Jordens Grænser for at høre Salomons Visdom; og se, her er mere end Salomon.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
Men når den urene Ånd er faren ud af Mennesket, vandrer den igennem vandløse Steder, søger Hvile og finder den ikke.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Da siger den: Jeg vil vende om til mit Hus, som jeg gik ud af; og når den kommer, finder den det ledigt, fejet og prydet.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Så går den hen og tager syv andre Ånder med sig, som ere værre end den selv, og når de ere komne derind, bo de der; og det sidste bliver værre med dette Menneske end det første. Således skal det også gå denne onde Slægt."
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
Medens han endnu talte til Skarerne, se, da stode hans Moder og hans Brødre udenfor og begærede at tale med ham.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
Da sagde en til ham: "Se, din Moder og dine Brødre stå udenfor og begære at tale med dig."
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
Men han svarede og sagde til den, som sagde ham det: "Hvem er min Moder? og hvem ere mine Brødre?"
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
Og han rakte sin Hånd ud over sine Disciple og sagde: "Se, her er min Moder og mine Brødre!
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
Thi enhver, der gør min Faders Villie, som er i Himlene, han er min Broder og Søster og Moder."

< Mattiyu 12 >