< Mattiyu 12 >
1 A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
V ten čas šel Ježíš v sobotu skrze obilí, učedlníci pak jeho lační jsouce, počali vymínati klasy a jísti.
2 Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
Farizeové pak spatřivše to, řekli jemu: Hle, učedlníci tvoji činí, čehož nesluší činiti v sobotu.
3 Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
On pak řekl jim: Co jste nečtli, co učinil David, když lačněl, on i ti, kteříž s ním byli?
4 Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
Kterak všel do domu Božího a chleby posvátné jedl, kterýchž jemu neslušelo jísti, ani těm, kteříž s ním byli, než toliko samým kněžím?
5 Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
Aneb zdali jste nečtli v zákoně, že kněží v sobotu v chrámě sobotu ruší, a jsou bez hříchu?
6 Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
Ale pravímť vám, že větší jest tuto nežli chrám.
7 Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
Než kdybyste věděli, co jest to: Milosrdenství chci a ne oběti, nepotupovali byste nevinných.
8 Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
Syn zajisté člověka jest pánem i soboty.
9 Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
A odšed odtud, přišel do školy jejich.
10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
A aj, byl tu člověk, maje ruku uschlou. I tázali se ho, řkouce: Sluší-li v sobotu uzdravovati? aby jej obžalovali.
11 Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
On pak dí jim: Který z vás bude člověk, ješto by měl ovci jednu, a kdyby ta upadla do jámy v sobotu, i zdaliž nedosáhne jí a nevytáhne?
12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
A čím lepší jest člověk než ovce? A protož slušíť v sobotu dobře činiti.
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
Tedy řekl člověku tomu: Vztáhni tu ruku svou. I vztáhl, a přivedena jest k zdraví jako druhá.
14 Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
Farizeové pak vyšedše, drželi radu proti němu, kterak by jej zahladili.
15 Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
A věděv to Ježíš, šel odtud. I šli za ním zástupové mnozí, a uzdravil je všecky.
16 yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
A s pohrůžkou přikázal jim, aby ho nezjevovali,
17 Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
Aby se naplnilo povědění skrze Izaiáše proroka, řkoucího:
18 “Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
Aj, služebník ten můj, kteréhož jsem vyvolil, ten milý můj, v němž se dobře zalíbilo duši mé. Položím Ducha svého na něj, a soud národům zvěstovati bude.
19 Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
Nebude se vaditi, ani křičeti, aniž kdo na ulicích uslyší hlas jeho.
20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
Třtiny nalomené nedolomí, a lnu kouřícího se neuhasí, až i vypoví soud k vítězství.
21 Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
A ve jménu jeho národové doufati budou.
22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
Tehdy přiveden k němu ďábelstvím posedlý, slepý a němý. I uzdravil jej, tak že ten slepý a němý i mluvil i viděl.
23 Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
I děsili se všickni zástupové a pravili: Není-liž tento ten Syn Davidův?
24 Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
Ale farizeové to uslyševše, řekli: Tento nevymítá ďáblů než skrze Belzebuba, kníže ďábelské.
25 Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
Ježíš pak znaje myšlení jejich, dí jim: Každé království rozdělené samo proti sobě spustne, a každé město neb dům proti sobě rozdělený nestane.
26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
A jestližeť satan satana vymítá, proti sobě rozdělen jest. Kterak tedy stane království jeho?
27 In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
A vymítám-liť já ďábly skrze Belzebuba, synové vaši skrze koho vymítají? Protož oni soudcové vaši budou.
28 Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
Pakliť já Duchem Božím ďábly vymítám, přišloť jest jistě mezi vás království Boží.
29 “Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
Aneb kterak kdo může do domu silného vjíti a jeho nádobí pobrati, leč by prvé svázal toho silného, a teprv by dům jeho obloupiti mohl?
30 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
Kdož není se mnou, proti mně jest; a kdo neshromažďuje se mnou, rozptylujeť.
31 Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
Protož pravím vám: Všeliký hřích i rouhání bude lidem odpuštěno, ale rouhání proti Duchu nebude odpuštěno lidem.
32 Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn )
A kdyby kdo řekl slovo proti Synu člověka, bude jemu odpuštěno, ale kdož by mluvil proti Duchu svatému, nebude jemu odpuštěno, ani v tomto věku, ani v budoucím. (aiōn )
33 “Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
Čiňtež aneb strom dobrý, i ovoce jeho dobré; aneb čiňte strom zlý, i ovoce jeho zlé. Neboť po ovoci strom bývá poznán.
34 Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
Pokolení ještěrčí, kterakž byste mohli dobré věci mluviti, jsouce zlí? Nebo z hojnosti srdce ústa mluví.
35 Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
Dobrý člověk z dobrého pokladu srdce vynáší dobré, a zlý člověk ze zlého pokladu vynáší zlé.
36 Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
Ale pravím vám, že z každého slova prázdného, kteréž mluviti budou lidé, vydadí počet v den soudný.
37 Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
Nebo z slov svých spravedliv budeš, a z řečí svých budeš odsouzen.
38 Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
Tehdy odpověděli někteří z zákonníků a farizeů, řkouce: Mistře, chceme od tebe znamení viděti.
39 Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
On pak odpovídaje, dí jim: Pokolení zlé a cizoložné znamení hledá, ale znamení jemu nebude dáno, jediné to znamení Jonáše proroka.
40 Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
Nebo jakož byl Jonáš v břiše velryba tři dni a tři noci, takť bude Syn člověka v srdci země tři dni a tři noci.
41 Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
Muži Ninivitští stanou na soudu s pokolením tímto, a potupí je, proto že pokání činili k Jonášovu kázaní, a aj, víceť nežli Jonáš tuto.
42 Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
Královna od poledne povstane k soudu s pokolením tímto, a potupí je; nebo přijela od končin země, aby slyšela moudrost Šalomounovu, a aj, víceť tuto nežli Šalomoun.
43 “Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
Když pak nečistý duch vyjde od člověka, chodí po místech suchých, hledaje odpočinutí, ale nenalézá.
44 Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
Tedy říká: Navrátím se do domu svého, odkudž jsem vyšel. A přijda, nalezne prázdný, vyčištěný a ozdobený.
45 Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
Tedy jde a vezme s sebou sedm jiných duchů horších, nežli jest sám, a vejdouce, přebývají tam, i bývají poslední věci člověka toho horší nežli první. Takť se stane i tomuto zlému pokolení.
46 Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
A když on ještě mluvil k zástupům, aj, matka a bratří jeho stáli vně, žádajíce s ním promluviti.
47 Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
I řekl jemu jeden: Aj, matka tvá i bratří tvoji stojí vně, chtíce s tebou mluviti.
48 Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
On pak odpovídaje, řekl tomu, kterýž jemu pověděl: Kdo jest matka má? A kdo jsou bratří moji?
49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
A vztáhna ruku svou na učedlníky své, řekl: Aj, matka má i bratří moji.
50 Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”
Nebo kdož by koli činil vůli Otce mého nebeského, ten jest bratr můj, i sestra má, i matka má.