< Mattiyu 11 >

1 Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya yi gaba daga can don yă koyar yă kuma yi wa’azi a garuruwan Galili.
And so it was, when Jesus finished directing His twelve disciples, that He moved on from there to teach and preach in their towns.
2 Sa’ad da Yohanna Mai Baftisma ya ji a kurkuku abin da Kiristi yake yi, sai ya aiki almajiransa
But John, hearing in prison about the works of the Messiah, sent two of his disciples
3 su tambaye shi, “Kai ne wanda zai zo, ko kuwa mu sa ido ga wani?”
to say to Him, “Are you the Coming One, or do we look for another?”
4 Yesu ya amsa ya ce, “Ku koma ku gaya wa Yohanna abin da kuka ji, kuka kuma gani.
By way of answer Jesus said to them: “Go and report to John the things that you hear and see:
5 Makafi suna gani, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin labari mai daɗi.
blind regain sight and lame walk, lepers are cleansed and deaf hear, dead are raised and the poor are evangelized.
6 Mai albarka ne mutumin da bai yi tuntuɓe ba saboda ni.”
And, blessed be whoever is not offended at Me!”
7 Sa’ad da almajiran Yohanna suke barin wurin, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna. “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
So as they departed Jesus began to say to the crowds concerning John: “What did you go out into the wilderness to see, a reed shaken by the wind?
8 In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da riguna masu kyau ne? A’a, masu sa riguna masu kyau, ai, a fadan sarakuna suke.
But what did you go out to see, a man clothed in soft garments? Actually, those who wear soft material are in kings' houses.
9 To, me kuka je kallo ne? Annabi? I, ina gaya muku, ya ma fi annabi.
But really, what did you go out to see, a prophet? Yes, I tell you, and far more than a prophet.
10 Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiki ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka a gabanka.’
For this is he of whom it is written: ‘Behold, I send my messenger before your face, who will prepare your way ahead of you.’
11 Gaskiya nake gaya muku. A cikin dukan waɗanda mata suka haifa, ba wani da ya taso da ya fi Yohanna Mai Baftisma girma; duk da haka mafi ƙanƙanta a mulkin sama ya fi shi girma.
Assuredly I say to you, among those born of women there has not arisen a greater than John the Baptizer; but he who is least in the kingdom of the heavens is greater than he.
12 Tun daga kwanakin Yohanna Mai Baftisma har yă zuwa yanzu, mulkin sama yana sha da ƙyar, fitanannu kuma sun kama mulkin sama sun riƙe gam.
But from the days of John the Baptizer until now the kingdom of the heavens is being aggressive and aggressive people are seizing upon it.
13 Gama dukan Annabawa da kuma Doka sun yi ta annabci har yă zuwa kan Yohanna.
For all the prophets and the Law prophesied until John,
14 In kuna niyya ku yarda da wannan, to, shi ne Iliya da dā ma zai zo.
and if you are willing to receive it, he is Elijah who is to come.
15 Duk mai kunnen ji, yă ji.
He who has ears to hear, let him hear!
16 “Da me zan kwatanta wannan zamani? Suna kama da yara da suke zaune a kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,
“But to what shall I compare this generation? It is like children sitting in a marketplace and calling to their friends
17 “‘Mun yi muku busa, ba ku kuwa yi rawa ba, mun rera waƙar makoki, ba ku kuwa yi makoki ba.’
and saying, ‘We played the flute for you and you did not dance; we mourned for you and you did not lament.’
18 Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo ba ya ciye-ciye, ba ya shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
For John came neither eating nor drinking and they say, ‘He has a demon’;
19 Ɗan Mutum ya zo yana ciye-ciye, yana shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama da kuma mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’ Amma akan tabbatar da hikima ta wurin ayyukanta.”
the Son of the Man came eating and drinking and they say, ‘Just look, a glutton and a drunkard, a friend of tax collectors and sinners!’ Indeed, wisdom is vindicated by her children.”
20 Sai Yesu ya fara yin tir da biranen da aka yi yawancin ayyukansa na banmamaki, don ba su tuba ba.
Then He began to reproach the cities in which most of His mighty works had been done, because they did not repent.
21 “Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida! Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba sanye da rigar makoki da toka.
“Woe to you, Chorazin! Woe to you, Bethsaida! Because if the mighty works that were done in you had been done in Tyre and Sidon, they would have repented long ago in sackcloth and ashes.
22 Amma ina gaya muku, za a fi jin tausayin Taya da Sidon a ranar shari’a, fiye da ku.
So I say to you, it will be more tolerable for Tyre and Sidon in the Day of judgment than for you!
23 Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. (Hadēs g86)
And you, Capernaum, ‘the one having been exalted to heaven’, you will be brought down to Hades! Because if the mighty works that were done in you had been done in Sodom, it would have remained until this day. (Hadēs g86)
24 Amma ina gaya miki, za a fi jin tausayin Sodom fiye da ke a ranar shari’a.”
So I say to you that it will be more tolerable for the land of Sodom in the Day of judgment than for you.”
25 A wannan lokaci sai Yesu ya ce, “Ina yabonka, Uba, Ubangijin sama da ƙasa, gama ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara.
At that time Jesus reacted and said: “‘I praise You, Father, Lord of heaven and earth, that You have hidden these things from the wise and intelligent and have revealed them to ‘babes’.
26 I, Uba, gama wannan shi ne abin da ka ji daɗin yi.
Yes, Father, because thus it was good to You.’
27 “Dukan kome Ubana ya danƙa mini. Ba wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban, sai dai Ɗan da kuma waɗanda Ɗan ya so yă bayyana musu shi.
“All things have been delivered to me by my Father, and no one really knows the Son except the Father; nor does anyone really know the Father except the Son, and the one to whom the Son may will to reveal Him.
28 “Ku zo gare ni, dukanku da kuka gaji kuke kuma fama da kaya, zan kuwa ba ku hutu.
Come to me all you who are laboring and are loaded down, and I will give you rest.
29 Ku ɗauki karkiyata a kanku, ku kuma yi koyi da ni, gama ni mai tawali’u ne marar girman kai, za ku kuwa sami hutu don rayukanku.
Take my yoke upon you and learn from me, because I am gentle and lowly in heart, and you will find rest for your souls;
30 Gama karkiyata mai sauƙi ce, kayana kuma marasa nauyi ne.”
for my yoke is easy and my burden is light.”

< Mattiyu 11 >