< Mattiyu 11 >
1 Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya yi gaba daga can don yă koyar yă kuma yi wa’azi a garuruwan Galili.
Hottelah a hnukkâbang hlaikahni touh hah kâ a poe hnukkhu, cangkhai hane hoi kamthang pâpho hanelah khopui khote tangkuem koe a cei.
2 Sa’ad da Yohanna Mai Baftisma ya ji a kurkuku abin da Kiristi yake yi, sai ya aiki almajiransa
Khrih ni a sak e pueng hah Baptisma kapoekung Jawhan ni thongim thung hoi a thai navah, amae a hnukkâbang kahni touh a patoun teh, a ka tho hane teh nang toung na maw.
3 su tambaye shi, “Kai ne wanda zai zo, ko kuwa mu sa ido ga wani?”
Hoehpawiteh alouke maw ka ngaihawi awh han rah, telah a pacei sak.
4 Yesu ya amsa ya ce, “Ku koma ku gaya wa Yohanna abin da kuka ji, kuka kuma gani.
Jisuh ni, Jawhan koe cet roi nateh na thai awh e hoi na hmu awh e pueng hah dei pouh awh, atipouh.
5 Makafi suna gani, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin labari mai daɗi.
Mit kadawnnaw ni kho a hmu awh toe. Kamkhuennaw ni lam a cei awh toe. Ka hrikbeinaw ni a thoung awh toe. Hnâpangnaw ni hnâ a thai awh toe. Kadoutnaw ni a thaw awh toe. Karoedengnaw ni hai lunghawinae kamthang a thai awh toe.
6 Mai albarka ne mutumin da bai yi tuntuɓe ba saboda ni.”
Kai kecu dawk a lung ka pout hoeh e teh a yawhawi telah atipouh.
7 Sa’ad da almajiran Yohanna suke barin wurin, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna. “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
Ahnimouh a cei a hnukkhu, Jisuh ni Jawhan deingainae lahoi rangpuinaw a dei pouh e teh, nangmouh ni bang hmu hane lahoi maw kahrawng na tâco a vaw. Kahlî ni hon a nawi e phonaw khet hanelah maw na tâco awh.
8 In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da riguna masu kyau ne? A’a, masu sa riguna masu kyau, ai, a fadan sarakuna suke.
Hoeh teh, khohna kahawi ka khohnat e khet hanelah maw na cei awh. Khohna kahawi ka khonaw teh siangpahrang im doeh ouk ao.
9 To, me kuka je kallo ne? Annabi? I, ina gaya muku, ya ma fi annabi.
Profet khet hanelah maw na cei awh. Bokheiyah. Profet hlak kalen e lah ka o ka ti.
10 Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiki ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka a gabanka.’
Cakathoung dawk thut e teh, khenhaw! na cei nahane lamthung ka rasoun hanelah kaie patoune hah na hmalah ka patoun ati navah ahni doeh a dei ngai nah.
11 Gaskiya nake gaya muku. A cikin dukan waɗanda mata suka haifa, ba wani da ya taso da ya fi Yohanna Mai Baftisma girma; duk da haka mafi ƙanƙanta a mulkin sama ya fi shi girma.
Atangcalah ka dei. Napui ni a khe e naw thung dawk Baptisma Jawhan hlak kalen e buet touh boehai kamphawng hoeh rah. Hatei, kalvan uknaeram dawkvah kathoungpounge hah ahni hlak a len han.
12 Tun daga kwanakin Yohanna Mai Baftisma har yă zuwa yanzu, mulkin sama yana sha da ƙyar, fitanannu kuma sun kama mulkin sama sun riƙe gam.
Baptisma Jawhan koehoi kamtawng teh atu totouh kalvan uknaeram hah a kâtuk awh. Kâtuk e naw ni hai thama lah a kâen awh.
13 Gama dukan Annabawa da kuma Doka sun yi ta annabci har yă zuwa kan Yohanna.
Jawhan a pha hoehnahlan totouh kâlawknaw hoi profet lawknaw ni na cangkhai awh.
14 In kuna niyya ku yarda da wannan, to, shi ne Iliya da dā ma zai zo.
Nangmouh ni ka lawk hah na thai panuek awh pawiteh ahni teh ka tho hane Elijah doeh toe.
15 Duk mai kunnen ji, yă ji.
Thai nahan hnâ ka tawn pueng ni thai naseh.
16 “Da me zan kwatanta wannan zamani? Suna kama da yara da suke zaune a kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,
Hete miphunnaw hah bang hoi maw ka bangnue han vai. Pawi koe ka tahung e camonaw hoi a kâvan awh.
17 “‘Mun yi muku busa, ba ku kuwa yi rawa ba, mun rera waƙar makoki, ba ku kuwa yi makoki ba.’
Kahawicalah ratoung tamawi ka tum a haiyah na lam awh hoeh. Khuika la sak nahaiyah na kap awh hoeh.
18 Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo ba ya ciye-ciye, ba ya shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
Jawhan teh catnet laipalah a tho navah, kahrai ni a man e doeh bout na ti awh.
19 Ɗan Mutum ya zo yana ciye-ciye, yana shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama da kuma mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’ Amma akan tabbatar da hikima ta wurin ayyukanta.”
Tami Capa teh canei laihoi a tho navah, ka carawng e, misurtui kâso e, tamuk kacawngnaw hoi tamikayonnaw e huiko lah kâsak e bout na ti pouh awh. Hateiteh, a lungangnae ni, a canaw a hlout sak telah a ti.
20 Sai Yesu ya fara yin tir da biranen da aka yi yawancin ayyukansa na banmamaki, don ba su tuba ba.
Hatnavah, athaonae a kamnue saknae khonaw ni pankângainae a tawn awh hoeh dawkvah, hote khonaw hah Jisuh ni a yue.
21 “Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida! Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba sanye da rigar makoki da toka.
Oe! Khorazin, na yawthoe. Bethsaida, na yawthoe. Nangmouh koe thaonae hno ka sak e naw hah Taire hoi Sidon khonaw dawkvah ka sak boipawiteh, hotnaw ni buri kâkhu hoi vaiphu kâphuen awh vaiteh, pankângai awh han ei nan toung mah.
22 Amma ina gaya muku, za a fi jin tausayin Taya da Sidon a ranar shari’a, fiye da ku.
Atangcalah na dei pouh awh, lawkcengnae hnin dawkvah, nangmouh teh Taire hoi Sidon khonaw hlak na khang awh han.
23 Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. (Hadēs )
Kapernuam kho, nang teh kalvan totouh tawm lah na kaawm ei nakunghai, phuen kho totouh pabo lah na o han. Na thungvah thaonae hno sak lah kaawm e naw hah Sodom kho dawkvah ka sak pawiteh, hote kho teh atu sittouh kangdout han ei. (Hadēs )
24 Amma ina gaya miki, za a fi jin tausayin Sodom fiye da ke a ranar shari’a.”
Atangcalah na dei pouh awh. Lawkcengnae hnin dawkvah Sodom kho hlak hoe na khang awh han, atipouh.
25 A wannan lokaci sai Yesu ya ce, “Ina yabonka, Uba, Ubangijin sama da ƙasa, gama ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara.
Hatnavah, Jisuh ni, kalvan hoi talai kaukkung a Pa, nang ni a lungkaangnaw hoi kathoumnaw koe kângairu hnonaw hah na hro teh, camonaw koe na pâpho dawkvah na lungmanae teh ka pholen.
26 I, Uba, gama wannan shi ne abin da ka ji daɗin yi.
Oe apa hottelah na ngainae ao.
27 “Dukan kome Ubana ya danƙa mini. Ba wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban, sai dai Ɗan da kuma waɗanda Ɗan ya so yă bayyana musu shi.
A Pa nang ni hnocawngca pueng kai koe na poe toe. Pa laipalah apinihai Capa panuek hoeh. Capa hoi Capa ni a kamnue pouh e hloilah apinihai Pa teh panuek hoeh.
28 “Ku zo gare ni, dukanku da kuka gaji kuke kuma fama da kaya, zan kuwa ba ku hutu.
Hno ka ri ni teh kapatangnaw kai koe tho awh, kai ni na kâhat sak han.
29 Ku ɗauki karkiyata a kanku, ku kuma yi koyi da ni, gama ni mai tawali’u ne marar girman kai, za ku kuwa sami hutu don rayukanku.
Kaie kahnam hah phawt awh. Kai koe kamtu awh. Kai teh lungdonae hoi lungnemnae lah ka o. Na hringnae ni kâhatnae a hmu han.
30 Gama karkiyata mai sauƙi ce, kayana kuma marasa nauyi ne.”
Bangkongtetpawiteh, kaie kahnam teh phu a nep. Ka hno hai a pâhaw, atipouh.