< Mattiyu 10 >

1 Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
Jésus, ayant appelé ses douze disciples, leur donna le pouvoir de chasser les esprits immondes et de guérir toutes sortes de maladies et toutes sortes d'infirmités.
2 Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
Or, voici les noms des douze apôtres: le premier est Simon, nommé Pierre, et André, son frère; Jacques, fils de Zébédée, et Jean, son frère;
3 Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
Philippe, et Barthélemi; Thomas, et Matthieu le péager; Jacques, fils d'Alphée, et Lebbée, surnommé Thaddée;
4 Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Simon le Cananite, et Judas l'Iscariote, qui même trahit Jésus.
5 Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
Jésus envoya ces douze-là, et il leur donna ses ordres, en disant: N'allez point vers les gentils, et n'entrez dans aucune ville des Samaritains;
6 A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
Mais allez plutôt vers les brebis perdues de la maison d'Israël.
7 Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
Et quand vous serez partis, prêchez, et dites: Le royaume des cieux approche.
8 Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
Guérissez les malades, nettoyez les lépreux, ressuscitez les morts, chassez les démons. Vous avez reçu gratuitement, donnez gratuitement.
9 “Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
Ne prenez ni or, ni argent, ni monnaie dans vos ceintures;
10 kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
Ni sac pour le voyage, ni deux habits, ni souliers, ni bâton; car l'ouvrier est digne de sa nourriture.
11 Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
Et dans quelque ville ou bourgade que vous entriez, informez-vous qui y est digne; et demeurez chez lui jusqu'à ce que vous partiez.
12 Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
Et quand vous entrerez dans quelque maison, saluez-la.
13 In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
Et si la maison en est digne, que votre paix vienne sur elle; mais si elle n'en est pas digne, que votre paix retourne à vous.
14 Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
Et partout où l'on ne vous recevra pas, et où l'on n'écoutera pas vos paroles, en sortant de cette maison ou de cette ville, secouez la poussière de vos pieds.
15 Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
Je vous dis en vérité que le sort de Sodome et de Gomorrhe sera plus supportable au jour du jugement que celui de cette ville-là.
16 “Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
Voici, je vous envoie comme des brebis au milieu des loups; soyez donc prudents comme les serpents, et simples comme les colombes.
17 Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
Mais soyez en garde contre les hommes; car ils vous livreront aux tribunaux, et ils vous feront fouetter dans les synagogues;
18 Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
Et vous serez menés devant les gouverneurs, et devant les rois, à cause de moi, pour rendre témoignage devant eux et devant les nations.
19 Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
Mais quand on vous livrera à eux, ne soyez point en peine ni de ce que vous direz, ni comment vous parlerez; car ce que vous aurez à dire vous sera inspiré à l'heure même.
20 gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
Car ce n'est pas vous qui parlerez, mais c'est l'Esprit de votre Père qui parlera en vous.
21 “Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
Or, le frère livrera son frère à la mort, et le père son enfant; et les enfants se soulèveront contre leurs pères et leurs mères, et les feront mourir.
22 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
Et vous serez haïs de tous à cause de mon nom; mais celui qui persévérera jusqu'à la fin, c'est celui-là qui sera sauvé.
23 Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
Or, quand ils vous persécuteront dans une ville, fuyez dans une autre; je vous dis en vérité que vous n'aurez pas achevé d'aller par toutes les villes d'Israël, que le Fils de l'homme ne soit venu.
24 “Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
Le disciple n'est pas plus que son maître, ni le serviteur plus que son seigneur.
25 Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
Il suffit au disciple d'être comme son maître, et au serviteur d'être comme son seigneur. S'ils ont appelé le père de famille Béelzébul, combien plus appelleront-ils ainsi ses domestiques?
26 “Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
Ne les craignez donc point; car il n'y a rien de caché qui ne doive être découvert, ni rien de secret qui ne doive être connu.
27 Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
Ce que je vous dis dans les ténèbres, dites-le dans la lumière; et ce que je vous dis à l'oreille, prêchez-le sur les toits.
28 Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
Et ne craignez point ceux qui ôtent la vie du corps, et qui ne peuvent faire mourir l'âme; mais craignez plutôt celui qui peut faire périr et l'âme et le corps dans la géhenne. (Geenna g1067)
29 Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
Deux passereaux ne se vendent-ils pas une pite? Or, il n'en tombera pas un seul à terre sans la permission de votre Père.
30 Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
Les cheveux même de votre tête sont tous comptés.
31 Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
Ne craignez donc rien; vous valez mieux que beaucoup de passereaux.
32 “Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
Quiconque donc me confessera devant les hommes, je le confesserai aussi devant mon Père qui est aux cieux.
33 Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
Mais quiconque me reniera devant les hommes, je le renierai aussi devant mon Père qui est aux cieux.
34 “Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
Ne pensez pas que je sois venu apporter la paix sur la terre: je suis venu apporter, non la paix, mais l'épée.
35 Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
Car je suis venu mettre la division entre le fils et le père, entre la fille et la mère, entre la belle-fille et la belle-mère.
36 abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
Et l'homme aura pour ennemis ceux de sa maison.
37 “Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
Celui qui aime son père ou sa mère plus que moi, n'est pas digne de moi; et celui qui aime son fils ou sa fille plus que moi, n'est pas digne de moi;
38 duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
Et celui qui ne prend pas sa croix, et ne me suit pas, n'est pas digne de moi.
39 Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
Celui qui aura conservé sa vie, la perdra; mais celui qui aura perdu sa vie à cause de moi, la retrouvera.
40 “Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
Celui qui vous reçoit, me reçoit; et celui qui me reçoit, reçoit celui qui m'a envoyé.
41 Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
Celui qui reçoit un prophète en qualité de prophète, recevra une récompense de prophète; et qui reçoit un juste en qualité de juste, recevra une récompense de juste.
42 In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”
Et quiconque aura donné à boire seulement un verre d'eau froide à un de ces petits, parce qu'il est mon disciple, je vous dis en vérité qu'il ne perdra point sa récompense.

< Mattiyu 10 >