< Mattiyu 10 >

1 Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
And having called to him his twelve disciples, he gave to them power over unclean spirits, so as to be casting them out, and to be healing every sickness, and every malady.
2 Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
And of the twelve apostles the names are these: first, Simon, who is called Peter, and Andrew his brother; James of Zebedee, and John his brother;
3 Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
Philip, and Bartholomew; Thomas, and Matthew the tax-gatherer; James of Alpheus, and Lebbeus who was surnamed Thaddeus;
4 Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Simon the Cananite, and Judas Iscariot, who did also deliver him up.
5 Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
These twelve did Jesus send forth, having given command to them, saying, 'To the way of the nations go not away, and into a city of the Samaritans go not in,
6 A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
and be going rather unto the lost sheep of the house of Israel.
7 Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
'And, going on, proclaim saying that, the reign of the heavens hath come nigh;
8 Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
infirm ones be healing, lepers be cleansing, dead be raising, demons be casting out — freely ye did receive, freely give.
9 “Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
'Provide not gold, nor silver, nor brass in your girdles,
10 kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
nor scrip for the way, nor two coats, nor sandals, nor staff — for the workman is worthy of his nourishment.
11 Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
'And into whatever city or village ye may enter, inquire ye who in it is worthy, and there abide, till ye may go forth.
12 Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
And coming to the house salute it,
13 In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
and if indeed the house be worthy, let your peace come upon it; and if it be not worthy, let your peace turn back to you.
14 Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
'And whoever may not receive you nor hear your words, coming forth from that house or city, shake off the dust of your feet,
15 Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
verily I say to you, It shall be more tolerable for the land of Sodom and Gomorrah in the day of judgment than for that city.
16 “Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
'Lo, I do send you forth as sheep in the midst of wolves, be ye therefore wise as the serpents, and simple as the doves.
17 Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
And, take ye heed of men, for they will give you up to sanhedrims, and in their synagogues they will scourge you,
18 Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
and before governors and kings ye shall be brought for my sake, for a testimony to them and to the nations.
19 Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
'And whenever they may deliver you up, be not anxious how or what ye may speak, for it shall be given you in that hour what ye shall speak;
20 gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
for ye are not the speakers, but the Spirit of your Father that is speaking in you.
21 “Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
'And brother shall deliver up brother to death, and father child, and children shall rise up against parents, and shall put them to death,
22 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
and ye shall be hated by all because of my name, but he who hath endured to the end, he shall be saved.
23 Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
'And whenever they may persecute you in this city, flee to the other, for verily I say to you, ye may not have completed the cities of Israel till the Son of Man may come.
24 “Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
'A disciple is not above the teacher, nor a servant above his lord;
25 Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
sufficient to the disciple that he may be as his teacher, and the servant as his lord; if the master of the house they did call Beelzeboul, how much more those of his household?
26 “Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
'Ye may not, therefore, fear them, for there is nothing covered, that shall not be revealed, and hid, that shall not be known;
27 Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
that which I tell you in the darkness, speak in the light, and that which you hear at the ear, proclaim on the house-tops.
28 Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
'And be not afraid of those killing the body, and are not able to kill the soul, but fear rather Him who is able both soul and body to destroy in gehenna. (Geenna g1067)
29 Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
'Are not two sparrows sold for an assar? and one of them shall not fall on the ground without your Father;
30 Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
and of you — even the hairs of the head are all numbered;
31 Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
be not therefore afraid, than many sparrows ye are better.
32 “Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
'Every one, therefore, who shall confess in me before men, I also will confess in him before my Father who is in the heavens;
33 Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
and whoever shall deny me before men, I also will deny him before my Father who is in the heavens.
34 “Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
'Ye may not suppose that I came to put peace on the earth; I did not come to put peace, but a sword;
35 Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
for I came to set a man at variance against his father, and a daughter against her mother, and a daughter-in-law against her mother-in-law,
36 abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
and the enemies of a man are those of his household.
37 “Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
'He who is loving father or mother above me, is not worthy of me, and he who is loving son or daughter above me, is not worthy of me,
38 duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
and whoever doth not receive his cross and follow after me, is not worthy of me.
39 Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
'He who found his life shall lose it, and he who lost his life for my sake shall find it.
40 “Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
'He who is receiving you doth receive me, and he who is receiving me doth receive Him who sent me,
41 Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
he who is receiving a prophet in the name of a prophet, shall receive a prophet's reward, and he who is receiving a righteous man in the name of a righteous man, shall receive a righteous man's reward,
42 In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”
and whoever may give to drink to one of these little ones a cup of cold water only in the name of a disciple, verily I say to you, he may not lose his reward.'

< Mattiyu 10 >