< Mattiyu 10 >

1 Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
Then He called to Him His twelve disciples and gave them authority over foul spirits, to drive them out; and to cure every kind of disease and infirmity.
2 Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
Now the names of the twelve Apostles were these: first, Simon called Peter, and his brother Andrew; James the son of Zabdi, and his brother John;
3 Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
Philip and Bartholomew, Thomas and Matthew the tax-gatherer, James the son of Alphaeus, and Thaddaeus;
4 Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Simon the Cananaean, and Judas the Iscariot, who also betrayed Him.
5 Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
These twelve Jesus sent on a mission, after giving them their instructions: "Go not," He said, "among the Gentiles, and enter no Samaritan town;
6 A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
but, instead of that, go to the lost sheep of Israel's race.
7 Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
And as you go, preach and say, 'The Kingdom of the Heavens is close at hand.'
8 Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
Cure the sick, raise the dead to life, cleanse lepers, drive out demons: you have received without payment, give without payment.
9 “Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
"Provide no gold, nor even silver nor copper to carry in your pockets;
10 kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
no bag for your journey, nor change of linen, nor shoes, nor stick; for the labourer deserves his food.
11 Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
"Whatever town or village you enter, inquire for some good man; and make his house your home till you leave the place.
12 Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
When you enter the house, salute it;
13 In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
and if the house deserves it, the peace you invoke shall come upon it. If not, your peace shall return to you.
14 Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
And whoever refuses to receive you or even to listen to your Message, as you leave that house or town, shake off the very dust from your feet.
15 Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
I solemnly tell you that it will be more endurable for the land of Sodom and Gomorrah on the day of Judgement than for that town.
16 “Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
"Remember it is I who am sending you out, as sheep into the midst of wolves; prove yourselves as sagacious as serpents, and as innocent as doves.
17 Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
But beware of men; for they will deliver you up to appear before Sanhedrins, and will flog you in their synagogues;
18 Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
and you will even be put on trial before governors and kings for my sake, to bear witness to them and to the Gentiles.
19 Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
But when they have delivered you up, have no anxiety as to how you shall speak or what you shall say; for at that very time it shall be given you what to say;
20 gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
for it is not you who will speak: it will be the Spirit of your Father speaking through you.
21 “Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
Brother will betray brother to death, and father, child; and children will rise against their own parents and will put them to death.
22 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
And you will be objects of universal hatred because you are called by my name; but he who holds out to the End--he will be saved.
23 Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
Whenever they persecute you in one town, escape to the next; for I solemnly tell you that you will not have gone the round of all the towns of Israel before the Son of Man comes.
24 “Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
"The learner is never superior to his teacher, and the servant is never superior to his master.
25 Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
Enough for the learner to be on a level with his teacher, and for the servant to be on a level with his master. If they have called the master of the house Baal-zebul, how much more will they slander his servants?
26 “Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
Fear them not, however; there is nothing veiled which will not be uncovered, nor secret which will not become known.
27 Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
What I tell you in the dark, speak in the light; and what is whispered into your ear, proclaim upon the roofs of the houses.
28 Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
"And do not fear those who kill the body, but cannot kill the soul; but rather fear him who is able to destroy both soul and body in Gehenna. (Geenna g1067)
29 Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
Do not two sparrows sell for a halfpenny? Yet not one of them will fall to the ground without your Father's leave.
30 Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
But as for you, the very hairs on your heads are all numbered.
31 Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
Away then with fear; you are more precious than a multitude of sparrows.
32 “Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
"Every man who acknowledges me before men I also will acknowledge before my Father who is in Heaven.
33 Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
But whoever disowns me before men I also will disown before my Father who is in Heaven.
34 “Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
"Do not suppose that I came to bring peace to the earth: I did not come to bring peace but a sword.
35 Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
For I came to set a man against his father, a daughter against her mother, and a daughter-in-law against her mother-in-law;
36 abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
and a man's own family will be his foes.
37 “Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
Any one who loves father or mother more than me is not worthy of me, and any one who loves son or daughter more than me is not worthy of me;
38 duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
and any one who does not take up his cross and follow where I lead is not worthy of me.
39 Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
To save your life is to lose it, and to lose your life for my sake is to save it.
40 “Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
"Whoever receives you receives me, and whoever receives me receives Him who sent me.
41 Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
Every one who receives a prophet, because he is a prophet, will receive a prophet's reward, and every one who receives a righteous man, because he is a righteous man, will receive a righteous man's reward.
42 In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”
And whoever gives one of these little ones even a cup of cold water to drink because he is a disciple, I solemnly tell you that he will not lose his reward."

< Mattiyu 10 >