< Mattiyu 10 >

1 Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
And he called to himself his twelve disciples, and gave them authority over unclean spirits, to cast them out, and to heal every disease and every sickness.
2 Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
Now the names of the twelve apostles are these. The first, Simon, who is called Peter; and Andrew his brother; and James the son of Zebedee, and John his brother;
3 Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
Philip and Bartholomew; Thomas and Matthew the tax collector; James the son of Alphaeus, and Thaddaeus;
4 Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Simon the Zealot, and Judas Iscariot, who also betrayed him.
5 Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
Jesus sent these twelve out, and commanded them, saying, "Do not go among the non-Jews, and do not enter into any city of the Samaritans.
6 A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
Rather, go to the lost sheep of the house of Israel.
7 Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
And as you go, proclaim, saying, 'The kingdom of heaven is near.'
8 Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
Heal the sick, raise the dead, cleanse the lepers, cast out demons. Freely you received, freely give.
9 “Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
Do not take any gold, nor silver, nor copper in your money belts.
10 kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
Take no bag for your journey, neither two tunics, nor shoes, nor staff: for the laborer is worthy of his food.
11 Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
And into whatever city or village you enter, find out who in it is worthy; and stay there until you go on.
12 Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
And as you enter into the household, greet it.
13 In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
And if the household is worthy, let your peace come on it, but if it is not worthy, let your peace return to you.
14 Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
And whoever does not receive you, nor hear your words, as you leave that house or that city, shake off the dust from your feet.
15 Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
Truly I tell you, it will be more tolerable for the land of Sodom and Gomorrah in the day of judgment than for that city.
16 “Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
"Look, I send you out as sheep in the midst of wolves, so be cunning as snakes and innocent as doves.
17 Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
But beware of people: for they will deliver you up to councils, and in their synagogues they will scourge you.
18 Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
Yes, and you will be brought before governors and kings for my sake, for a testimony to them and to the nations.
19 Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
But when they deliver you over, do not be anxious how or what you will say, for it will be given you in that hour what you will say.
20 gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
For it is not you who speak, but the Spirit of your Father who speaks in you.
21 “Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
"And brother will deliver up brother to death, and the father his child. Children will rise up against parents, and cause them to be put to death.
22 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
And you will be hated by everyone because of my name, but the one who perseveres to the end will be saved.
23 Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
But when they persecute you in one city, flee to the other. And if they persecute you in the other, flee to the next. For truly I tell you, you will not have gone through the cities of Israel before the Son of Man comes.
24 “Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
"A disciple is not above the teacher, nor a servant above his lord.
25 Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
It is enough for the disciple that he be like his teacher, and the servant like his lord. If they have called the master of the house Beelzebul, how much more those of his household.
26 “Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
Therefore do not be afraid of them, for there is nothing covered that will not be revealed; and hidden that will not be known.
27 Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
What I tell you in the darkness, speak in the light; and what you hear whispered in the ear, proclaim on the housetops.
28 Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
And do not be afraid of those who kill the body, but are not able to kill the soul. Rather, fear him who is able to destroy both soul and body in hell. (Geenna g1067)
29 Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
"Are not two sparrows sold for an assarion coin? Not one of them falls on the ground apart from your Father's will,
30 Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
but the very hairs of your head are all numbered.
31 Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
Therefore do not be afraid. You are of more value than many sparrows.
32 “Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
Everyone therefore who confesses me before people, him I will also confess before my Father who is in heaven.
33 Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
But whoever denies me before people, him I will also deny before my Father who is in heaven.
34 “Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
"Do not think that I came to send peace on the earth. I did not come to send peace, but a sword.
35 Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
For I came to set a man at odds against his father, and a daughter against her mother, and a daughter-in-law against her mother-in-law.
36 abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
And a person's foes will be those of his own household.
37 “Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
Whoever loves father or mother more than me is not worthy of me; and whoever loves son or daughter more than me is not worthy of me.
38 duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
And whoever does not take his cross and follow after me, is not worthy of me.
39 Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
Whoever seeks his life will lose it; and whoever loses his life for my sake will find it.
40 “Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
Whoever receives you receives me, and whoever receives me receives him who sent me.
41 Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
The one who receives a prophet because he is a prophet will receive a prophet's reward, and the one who receives a righteous person because he is a righteous person will receive a righteous person's reward.
42 In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”
And whoever gives one of these little ones just a cup of cold water to drink because he is a disciple, truly I tell you he will in no way lose his reward."

< Mattiyu 10 >