< Mattiyu 10 >

1 Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
So summoning His twelve disciples He gave them authority over unclean spirits so as to cast them out, and to heal every disease and every illness.
2 Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
Now the names of the twelve apostles are these: first Simon (the one called Peter) and Andrew his brother, James (the son of Zebedee) and John his brother,
3 Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
Philip and Bartholomew, Thomas and Matthew (the tax collector), James (the son of Alphaeus) and Lebbaeus (who was surnamed Thaddeus),
4 Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Simon (the Canaanite) and Judas Iscariot (who also betrayed Him).
5 Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
These twelve Jesus sent out, and commanded them saying: “Do not go off into the road of the Gentiles, and do not enter a city of the Samaritans.
6 A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
But go rather to the lost sheep of the house of Israel.
7 Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
And as you go, preach, saying, ‘The kingdom of the heavens has come near.’
8 Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
Heal the sick, cleanse the lepers, cast out demons. You have received free of charge, give free of charge.
9 “Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
Do not provide gold nor silver nor copper in your money belts,
10 kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
nor a knapsack for the road, nor two tunics, nor sandals, nor staffs; because the worker is worthy of his food.
11 Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
“In whatever city or village you may enter, inquire who in it is worthy, and stay there until you go out.
12 Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
Upon entering the house, greet it;
13 In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
and should the house be worthy, let your peace come upon it; but should it not be worthy, let your peace return to you.
14 Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
And whoever will not receive you nor hear your words, as you go out from that house or city shake off the dust from your feet.
15 Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
Assuredly I say to you, it will be more tolerable for the land of Sodom and Gomorrah in the Day of judgment than for that city!
16 “Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
“Now then, I am sending you out like sheep in the midst of wolves. Therefore be prudent like snakes and innocent like doves.
17 Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
But beware of the people, for they will hand you over to councils and flog you in their synagogues.
18 Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
And you will be brought before governors and even kings for my sake, as a testimony to them and to the nations.
19 Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
But whenever they hand you over, do not worry about how or what you will speak, for it will be given to you in that hour what you should speak;
20 gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
for it is not you who speak, but the Spirit of your Father who speaks in you.
21 “Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
“Furthermore, brother will hand over brother to death, and a father a child, and children will rise up against parents and put them to death.
22 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
And you will be hated by all for my name's sake; but the one enduring to the end, he will be delivered.
23 Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
But whenever they persecute you in this city, flee to another. For assuredly I say to you, you will certainly not go through all the cities of Israel before the Son of the Man comes.
24 “Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
A disciple is not above his teacher, nor a slave above his master.
25 Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
It is enough for a disciple that he become like his teacher, and a slave like his master. Since they have stigmatized the master of the house as Beelzebul, how much more those of his household!
26 “Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
So do not fear them; because there is nothing concealed that will not be revealed, and secret that will not be known.
27 Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
“What I tell you in the dark, say in the light; and what you hear in the ear, proclaim on the housetops.
28 Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
And do not be afraid of those who kill the body but cannot kill the soul. But rather fear the One who is able to destroy both soul and body in Hell. (Geenna g1067)
29 Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
Are not two sparrows sold for a copper coin? Yet not one of them will fall to the ground apart from your Father's will.
30 Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
Why even the hairs of your head are all numbered!
31 Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
Therefore do not be afraid; you are worth more than many sparrows.
32 “Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
“Now then, everyone who will confess me before the people, I will also confess him before my Father who is in the heavens.
33 Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
But whoever should deny me before the people, I will also deny him before my Father who is in the heavens.
34 “Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
“Do not suppose that I came to bring peace on the earth. I did not come to bring peace, but a sword.
35 Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
For I came to set a man against his father, and a daughter against her mother, and a daughter-in-law against her mother-in-law;
36 abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
and a man's enemies will be those of his own household.
37 “Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
“The one who is more devoted to father or mother than to me is not worthy of me, and the one who is more devoted to son or daughter than to me is not worthy of me;
38 duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
and he who does not take up his cross and follow after me is not worthy of me.
39 Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
The one ‘finding’ his life will lose it, and the one ‘losing’ his life for my sake will find it.
40 “Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
“The one receiving you receives me, and the one receiving me receives the One who sent me.
41 Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
The one receiving a prophet in the name of a prophet will receive a prophet's reward, and the one receiving a righteous man in the name of a righteous man will receive a righteous man's reward.
42 In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”
And whoever should give so much as a cup of cold water to one of these little ones, in the name of a disciple, assuredly I say to you, he will certainly not lose his reward.”

< Mattiyu 10 >