< Mattiyu 10 >
1 Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
Og han kaldte sine tolv Disciple til sig og gav dem Magt over urene Aander, til at uddrive dem og at helbrede enhver Sygdom og enhver Skrøbelighed.
2 Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
Og disse ere de tolv Apostles Navne: Først Simon, som kaldes Peter, og Andreas, hans Broder, og Jakob, Zebedæus's Søn, og Johannes, hans Broder,
3 Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
Filip og Bartholomæus, Thomas og Tolderen Matthæus, Jakob, Alfæus's Søn, og Lebbæus med Tilnavn Thaddæus,
4 Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Simon Kananæeren og Judas Iskariot, han, som forraadte ham.
5 Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
Disse tolv udsendte Jesus, bød dem og sagde: „Gaar ikke hen paa Hedningers Vej, og gaar ikke ind i Samaritaners By!
6 A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
Men gaar hellere hen til de fortabte Faar af Israels Hus!
7 Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
Men paa eders Vandring skulle I prædike og sige: Himmeriges Rige er kommet nær.
8 Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
Helbreder syge, opvækker døde, renser spedalske, uddriver onde Aander! I have modtaget det for intet, giver det for intet!
9 “Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
Skaffer eder ikke Guld, ej heller Sølv, ej heller Kobber i eders Bælter;
10 kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
ej Taske til at rejse med, ej heller to Kjortler, ej heller Sko, ej heller Stav; thi Arbejderen er sin Føde værd.
11 Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
Men hvor I komme ind i en By eller Landsby, der skulle I spørge, hvem i den der er det værd, og der skulle I blive, indtil I drage bort.
12 Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
Men naar I gaa ind i Huset, da hilser det;
13 In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
og dersom Huset er det værd, da komme eders Fred over det; men dersom det ikke er det værd, da vende eders Fred tilbage til eder!
14 Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
Og dersom nogen ikke modtager eder og ej hører eders Ord, da gaar ud af det Hus eller den By og ryster Støvet af eders Fødder!
15 Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
Sandelig, siger jeg eder, det skal gaa Sodomas og Gomorras Land taaleligere paa Dommens Dag end den By.
16 “Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
Se, jeg sender eder som Faar midt iblandt Ulve; vorder derfor snilde som Slanger og enfoldige som Duer!
17 Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
Vogter eder for Menneskene; thi de skulle overgive eder til Raadsforsamlinger og hudstryge eder i deres Synagoger.
18 Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
Og I skulle føres for Landshøvdinger og Konger for min Skyld, dem og Hedningerne til et Vidnesbyrd.
19 Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
Men naar de overgive eder, da bekymrer eder ikke for, hvorledes eller hvad I skulle tale; thi det skal gives eder i den samme Time, hvad I skulle tale.
20 gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
Thi I ere ikke de, som tale; men det er eders Faders Aand, som taler i eder.
21 “Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
Men Broder skal overgive Broder til Døden, og Fader sit Barn, og Børn skulle sætte sig op imod Forældre og slaa dem ihjel.
22 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
Og I skulle hades af alle for mit Navns Skyld; men den, som holder ud indtil Enden, han skal blive frelst.
23 Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
Men naar de forfølge eder i een By, da flyr til en anden; thi sandelig, siger jeg eder, I skulle ikke komme til Ende med Israels Byer, førend Menneskesønnen kommer.
24 “Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
En Discipel er ikke over sin Mester, ej heller en Tjener over sin Herre.
25 Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
Det er Discipelen nok, at han bliver som sin Mester, og Tjeneren som sin Herre. Have de kaldet Husbonden Beelzebul, hvor meget mere da hans Husfolk?
26 “Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
Frygter altsaa ikke for dem; thi intet er skjult, som jo skal aabenbares, og intet er lønligt, som jo skal blive kendt.
27 Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
Taler i Lyset, hvad jeg siger eder i Mørket; og prædiker paa Tagene, hvad der siges eder i Øret!
28 Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna )
Og frygter ikke for dem, som slaa Legemet ihjel, men ikke kunne slaa Sjælen ihjel; men frygter hellere for ham, som kan fordærve baade Sjæl og Legeme i Helvede. (Geenna )
29 Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
Sælges ikke to Spurve for en Penning? Og ikke een af dem falder til Jorden uden eders Faders Villie.
30 Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
Men paa eder ere endog alle Hovedhaar talte.
31 Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
Frygter derfor ikke; I ere mere værd end mange Spurve.
32 “Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
Altsaa, enhver som vedkender sig mig for Menneskene, ham vil ogsaa jeg vedkende mig for min Fader, som er i Himlene.
33 Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
Men den, som fornægter mig for Menneskene, ham vil ogsaa jeg fornægte for min Fader, som er i Himlene.
34 “Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
Mener ikke, at jeg er kommen for at bringe Fred paa Jorden; jeg er ikke kommen for at bringe Fred, men Sværd.
35 Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
Thi jeg er kommen for at volde Splid imellem en Mand og hans Fader og imellem en Datter og hendes Moder og imellem en Svigerdatter og hendes Svigermoder,
36 abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
og en Mands Husfolk skulle være hans Fjender.
37 “Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
Den, som elsker Fader eller Moder mere end mig, er mig ikke værd; og den, som elsker Søn eller Datter mere end mig, er mig ikke værd;
38 duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
og den, som ikke tager sit Kors og følger efter mig, er mig ikke værd.
39 Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
Den, som bjærger sit Liv, skal miste det; og den, som mister sit Liv for min Skyld, skal bjærge det.
40 “Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
Den, som modtager eder, modtager mig; og den, som modtager mig, modtager ham, som udsendte mig.
41 Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
Den, som modtager en Profet, fordi han er en Profet, skal faa en Profets Løn; og den, som modtager en retfærdig, fordi han er en retfærdig, skal faa en retfærdigs Løn.
42 In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”
Og den, som giver en af disse smaa ikkun et Bæger koldt Vand at drikke, fordi han er en Discipel, sandelig, siger jeg eder, han skal ingenlunde miste sin Løn.”