< Mattiyu 1 >
1 Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
Imbuka ya luzuvo lwa Jesu Kereste mwana wa Daafita mwana wa Abrahama.
2 Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
Abrahama a vali nji si wa Isaka, ni Isaka isi wa Jakobo, ni Jakobo isi wa Juda ni vance.
3 Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
Juda a vali njisi wa Perezi ni Zera cha Tama, Perezi isi wa Hezironi, ni Hezironi isi wa Ramu.
4 Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Ramu a vali njisi wa Amminadab, Amminadab isi wa Nahshoni, ni Nahshoni isi wa Salumoni.
5 Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
Salumoni ivali nji si wa Boazi cha Rahaba, Boazi isi wa Obedi cha Ruti, Obedi isi wa Jesse,
6 Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
Jesse a vali nji si wa Daafita simwine. Daafita a vali njisi Solomoni cha mwihyavwe wa Uriya.
7 Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
Solomoni a vali nji si wa Rehoboamu, Rehoboamu isi wa Abijah, Abijah isi wa Asa.
8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
Asa a vali njisi wa Josafati, Josafati isi wa Joramu, ni Joramu isi wa Uzziah.
9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
Uzziya avali njisi wa Jotamu, Jotamu isi wa Ahazi, Ahazi isi wa Hezekiya.
10 Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
Hezekiya a vali njisi wa Manasseh, Mannasseh isi wa Amoni, ni Amoni isi wa Josiyah.
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
Josiya avali njisi wa Jekoniya ni vanche he nako i vavaka luwitwe kwa Bavilona.
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
Mi kuzwa ha kuka luwiwa kwa Babilona, Jekoniya a vali njisi wa Salatiele, Salatiele a vali muzimu wa Zerubabele.
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
Zerubabele a vali njisi wa Abiudi, Abiudi isi wa Eliyakimu, ni Eliyakimu isi wa Azoro.
14 Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
Azoro a vali njisi wa Zadoki, Zadoki isi wa Akimu, ni Akimu isi wa Eliudu.
15 Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
Eliudi avali nji si wa Eliyazere, Eliyazere isi wa Matani, ni Matani isi wa Jakobo.
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
Jokobo avali nji si wa Josefa mwihyabwe wa Maria, kakwe Jesu na zalwa, yo sumpwa Keresite.
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
Mahasi onse ku zwa kwa Abrahama ku ya kwa Daafita a vali mahasi ena ikumi lyonke ni one, kuzwa kwa Daafita kuya ha vaka luwiwa kwa Babilona ku leta kwa Keresite avali masika ena ikumi lyonke ni one.
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
Ku zalwa kwa Jesu Keresite kuva chitahali mu nzila i chilila. Inyina, Maria, ava veelezwe kuti a seswe kwa Josefa, kono pili ni vaseni kwiza hamwina, ava waniki ha menzi mahya cha Luhuho lu Jolola.
19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
Mwihyavwe, Josefa, avali mukwane yo shiyeme, kono kana a vali kusaka ku shuvulisa mwihyabve iñandaleza. Cwale cha nahana ku manisa che nkunutu ku li veereza kwaakwe naye.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
Havali kusi nahana cezi zintu, Iñeloi lya Ireza ni lya livonisa kwali mu chiloto, liti, “Josefa, mwana wa Daafita, kanji u tiyi to hinda Maria kuva muhwenu, kakuli yo lihinditwe kwali avali ku lihindwa cha Luhuho lu Jolola.
21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
Mwa zale mwana' mushisu, mi momu ulike izina lya Jesu, mukuti ka puluse vantu vakwe ku zivi zavo.”
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
Izo zonse zi va pangahali kwi zuziliza chiva wambiwa kwa Simwine cha muporofita, nati,
23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
“Mu vone, mwalyango mwave ha menzi mahya, mi mwa zale mwana' shwisu, mi mu va mu sumpe izina lyakwe Imanuere”- i talusa, “Ireza wina neswe.”
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
Josefa ha vuka ku ñonzi zakwe ni ku chita ka kuya ke Iñeloi lya Simwine muli va mu laeli mi ca mu hinda kuva mwihyavwe.
25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
Kono kana aba lali naye konji ha zala mwana' mushisu. Mi ava mu sumpisi izina lya Jesu.