< Mattiyu 1 >
1 Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
Ma e kaka anywola mar Yesu Kristo ma wuod Daudi kendo wuod Ibrahim chalo:
2 Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
Ibrahim ne en wuon Isaka, Isaka ne en wuon Jakobo, to Jakobo ne en wuon Juda gi owetene.
3 Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
Juda ne en wuon Perez gi Zera, ma min-gi ne en Tamar, Perez ne en wuon Hezron, Hezron ne en wuon Ram,
4 Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
to Ram ne en wuon Aminadab. Aminadab ne en wuon Nashon, Nashon ne en wuon Salmon,
5 Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
Salmon ne en wuon Boaz, ma min-gi ne en Rahab. Boaz ne en wuon Obed ma min-gi ne en Ruth, Obed ne en wuon Jesse,
6 Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
to Jesse ne en wuon Ruoth Daudi. Daudi ne en wuon Solomon, ma min-gi, kane pok Daudi okawe, ne en chi Uria,
7 Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
Solomon ne en wuon Rehoboam, Rehoboam ne en wuon Abija, to Abija ne en wuon Asa.
8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
Asa ne en wuon Jehoshafat, Jehoshafat ne en wuon Jehoram, Jehoram ne en wuon Uzia,
9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
to Uzia ne en wuon Jotham, Jotham ne en wuon Ahaz, Ahaz ne en wuon Hezekia,
10 Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
to Hezekia ne en wuon Manase. Manase ne en wuon Amon, Amon ne en wuon Josia,
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
kendo Josia ne en wuon Jekonia gi owetene, e kinde mag twech e piny Babulon.
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
Bangʼ twech e Babulon: Jekonia ne en wuon Shealtiel, Shealtiel ne en wuon Zerubabel,
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
Zerubabel ne en wuon Abihud, to Abihud ne en wuon Eliakim. Eliakim ne en wuon Azor,
14 Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
Azor ne en wuon Zadok, Zadok ne en wuon Akim, to Akim ne en wuon Eliud.
15 Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
Eliud ne en wuon Eleazar, Eleazar ne en wuon Mathan, Mathan ne en wuon Jakobo,
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
to Jakobo ne en wuon Josef mane chwor Maria mane onywolo Yesu, miluongo ni Kristo.
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
Kamano tienge duto mane nitie chakre Ibrahim nyaka Daudi ne gin apar gangʼwen; to chakre Daudi nyaka ndalo twech e Babulon ne tienge apar gangʼwen kendo chakre ndalo twech nyaka kinde mag Kristo bende ne tienge apar gangʼwen.
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
Kama e kaka nywol mar Yesu Kristo notimore: Noyudo min mare ma Maria osesingi ne Josef mondo okende, to kane pok gibedo kaachiel, noyude ka en gi ich kuom Roho Maler.
19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
Nikech Josef chwore ne en ngʼat makare, kendo ne ok odwar ni okuod wiye e nyim ji, omiyo nochano e pache mar weye ma lingʼ-lingʼ.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
To bangʼ paro mar timo kamano, Malaika mar Ruoth nofwenyorene e lek mowachone niya, “Josef wuod Daudi, kik iluor dhi gi Maria dala kaka chiegi, nikech gima otingʼo e iye owuok kuom Roho Maler.
21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
Obiro nywolo wuowi, kendo nyaka imiye nying ni Yesu, nikech obiro waro joge kogolo e richo.”
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
Magi duto notimore mondo ochop gima ne Ruoth owacho gi dho janabi niya,
23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
“Nyako ngili biro mako ich minywol wuowi, mi nigiluonge ni Imanuel” (tiende ni, “Nyasaye ni kodwa”).
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
Kane Josef ochiewo gokinyi, notimo gima malaika mar Ruoth nochike mondo otim, kendo nokawo Maria odhigo dala mobedo chiege.
25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
To ne ok oriwore kode nyaka bangʼ kane osenywolo nyathi ma wuowi kendo nomiye nying ni Yesu.