< Markus 9 >

1 Ya kuma ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
Il leur dit aussi: Je vous dis en vérité, qu'il y en a quelques-uns de ceux qui sont ici présents, qui ne mourront point, qu'ils n'aient vu le royaume de Dieu venir avec puissance.
2 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna tare da shi, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, suka kasance su kaɗai a wurin. A can aka sāke kamanninsa a gabansu.
Six jours après, Jésus prit avec lui Pierre, Jacques et Jean, et les mena seuls à part sur une haute montagne; et il fut transfiguré en leur présence.
3 Tufafinsa suka zama fari suna ƙyalli, fiye da yadda wani a duniya zai iya yi su.
Et ses vêtements devinrent resplendissants, blancs comme la neige et tels qu'il n'y a point de foulon sur la terre qui pût ainsi blanchir.
4 Iliya da Musa suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
Et ils virent paraître Moïse et Élie, qui s'entretenaient avec Jésus.
5 Bitrus ya ce wa Yesu, “Rabbi, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Alors Pierre, prenant la parole, dit à Jésus: Maître, il est bon que nous demeurions ici; faisons donc trois tentes, une pour toi, une pour Moïse, et une pour Élie.
6 (Bai san abin da zai faɗa ba ne, gama sun tsorata ƙwarai.)
Car il ne savait pas ce qu'il disait, parce qu'ils étaient effrayés.
7 Sai wani girgije ya bayyana, ya rufe su, wata murya kuma ta fito daga girgijen, ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna, ku saurare shi!”
Et il vint une nuée qui les couvrit; et une voix sortit de la nuée, qui dit: C'est ici mon Fils bien-aimé, écoutez-le.
8 Farat ɗaya, da suka waiwaya, ba su ƙara ganin kowa tare da su ba, sai dai Yesu.
Et soudain les disciples, ayant regardé autour d'eux, ne virent plus personne que Jésus seul avec eux.
9 Da suna saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.
Et comme ils descendaient de la montagne, il leur défendit de dire à personne ce qu'ils avaient vu, jusqu'à ce que le Fils de l'homme fût ressuscité des morts.
10 Suka riƙe wannan zance a ɓoye tsakaninsu, suna tattaunawa ko mece ce ma’anar “tashi daga matattu.”
Et ils retinrent cette parole, se demandant les uns aux autres ce que voulait dire, ressusciter des morts.
11 Suka tambaye shi, suka ce, “Don me malaman dokoki suke cewa, sai Iliya ya fara zuwa?”
Et ils l'interrogeaient, en disant: Pourquoi les scribes disent-ils qu'il faut qu'Élie vienne premièrement?
12 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya ne, Iliya zai zo da fari, yă kuma mayar da dukan abubuwa. Don me kuma aka rubuta cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahala sosai, kuma a ƙi shi?
Il leur répondit: Il est vrai qu'Élie doit venir premièrement et rétablir toutes choses; et que le Fils de l'homme, selon qu'il est écrit de lui, doit souffrir beaucoup, et être méprisé.
13 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, kuma suka yi duk abin da suka ga dama da shi, kamar yadda aka rubuta game da shi.”
Mais je vous dis qu'Élie est venu, et qu'ils lui ont fait tout ce qu'ils ont voulu, comme il est écrit de lui.
14 Da suka dawo wurin sauran almajiran, sai suka ga babban taro kewaye da su, malaman dokoki suna gardama da su.
Et étant venu vers les autres disciples, il vit une grande foule autour d'eux, et des scribes qui disputaient avec eux.
15 Nan take da dukan mutanen suka ga Yesu, sai suka cika da mamaki, suka ruga da gudu don su gai da shi.
Et dès que toute cette foule le vit, elle fut saisie d'étonnement, et étant accourus ils le saluèrent.
16 Ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi da su?”
Alors il demanda aux scribes: De quoi disputez-vous avec eux?
17 Wani mutum a cikin taron ya amsa ya ce, “Malam, na kawo maka ɗana mai wani ruhun da yake hana shi magana.
Et un homme de la foule, prenant la parole, dit: Maître, je t'ai amené mon fils qui est possédé d'un esprit muet.
18 Duk lokacin da mugun ruhun ya kama shi, yakan jefa shi a ƙasa. Bakinsa yakan yi kumfa, yă cije haƙorarsa, yakan sa jikinsa ya sandare, yă zama da ƙarfi. Na roƙi almajiranka su fitar da ruhun, amma ba su iya ba.”
En quelque lieu qu'il le saisisse, il le déchire; et il écume, il grince les dents, et se dessèche; et j'ai prié tes disciples de le chasser; mais ils ne l'ont pu.
19 Yesu ya ce, “Ya ku zamani marar bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron.”
Alors Jésus leur répondit: O race incrédule, jusqu'à quand serai-je avec vous? jusqu'à quand vous supporterai-je? Amenez-le-moi.
20 Sai suka kawo shi. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan sai ya buge yaron da farfaɗiya. Ya fāɗi a ƙasa, yana birgima, bakinsa yana kumfa.
Ils le lui amenèrent donc; et dès qu'il vit Jésus, l'esprit l'agita avec violence, et il tomba par terre, et se roulait en écumant.
21 Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe yake haka?” Ya ce, “Tun yana ƙarami.
Alors Jésus demanda à son père: Combien y a-t-il de temps que ceci lui arrive? Le père dit: Dès son enfance.
22 Ya sha jefa shi cikin wuta, ko ruwa don yă kashe shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”
Et l'esprit l'a souvent jeté dans le feu et dans l'eau, pour le faire périr; mais si tu y peux quelque chose, aide-nous et aie compassion de nous.
23 Yesu ya ce, “‘In za ka iya’? Ai, kome mai yiwuwa ne ga wanda ya gaskata.”
Jésus lui dit: Si tu peux croire, toutes choses sont possibles pour celui qui croit.
24 Nan da nan mahaifin yaron ya faɗa da ƙarfi ya ce, “Na gaskata, ka taimake ni in sha kan rashin bangaskiyata!”
Aussitôt le père de l'enfant s'écriant, dit avec larmes: Je crois, Seigneur, aide-moi dans mon incrédulité.
25 Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
Et Jésus voyant que le peuple accourait en foule, reprit sévèrement l'esprit immonde et lui dit: Esprit muet et sourd, je te l'ordonne, moi, sors de cet enfant, et ne rentre plus en lui.
26 Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
Et l'esprit sortit en jetant un grand cri et en l'agitant avec violence; et l'enfant devint comme mort, de sorte que plusieurs disaient: Il est mort.
27 Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
Mais Jésus, l'ayant pris par la main, le fit lever; et il se tint debout.
28 Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
Lorsque Jésus fut entré dans la maison, ses disciples lui demandèrent en particulier: Pourquoi n'avons-nous pas pu chasser ce démon?
29 Ya amsa ya ce, “Sai da addu’akaɗai irin wannan yakan fita.”
Et il leur répondit: Cette espèce de démons ne peut sortir que par la prière et le jeûne.
30 Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yă san inda suke ba,
Puis étant partis de là, ils traversèrent la Galilée; et Jésus ne voulut pas que personne le sût.
31 gama yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.”
Cependant il instruisait ses disciples, et il leur disait: Le Fils de l'homme va être livré entre les mains des hommes, et ils le feront mourir; mais après avoir été mis à mort, il ressuscitera le troisième jour.
32 Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan.
Mais ils ne comprenaient point ce discours; et ils craignaient de l'interroger.
33 Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
Il vint ensuite à Capernaüm; et étant dans la maison, il leur demanda: De quoi discouriez-vous ensemble en chemin?
34 Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma?
Et ils se turent; car ils avaient disputé en chemin, sur celui qui serait le plus grand.
35 Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun ya ce, “In wani yana so yă zama na fari, dole yă zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.”
Et s'étant assis, il appela les douze et leur dit: Si quelqu'un veut être le premier, il sera le dernier de tous et le serviteur de tous.
36 Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yă tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu,
Et ayant pris un petit enfant, il le mit au milieu d'eux; et le tenant entre ses bras, il leur dit:
37 “Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”
Quiconque reçoit un de ces petits enfants à cause de mon nom, me reçoit; et quiconque me reçoit, ce n'est pas moi qu'il reçoit, mais celui qui m'a envoyé.
38 Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yă daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.”
Alors Jean, prenant la parole, lui dit: Maître, nous avons vu quelqu'un chasser les démons en ton nom et qui ne nous suit pas, et nous nous y sommes opposés, parce qu'il ne nous suit pas.
39 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yă faɗi wani abu mummuna game da ni.
Mais Jésus dit: Ne vous y opposez point; car il n'y a personne qui fasse des miracles en mon nom, et qui puisse aussitôt parler mal de moi.
40 Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.
Car celui qui n'est pas contre nous, est pour nous.
41 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba.
Et quiconque vous donnera un verre d'eau en mon nom, parce que vous appartenez à Christ, je vous dis en vérité, qu'il ne perdra pas sa récompense;
42 “Idan kuma wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan’yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku.
Mais quiconque scandalisera l'un de ces petits qui croient en moi, il vaudrait mieux pour lui qu'on lui mît une meule au cou, et qu'on le jetât dans la mer.
43 In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna g1067)
Que si ta main te fait tomber, coupe-la; il vaut mieux pour toi que tu entres dans la vie, n'ayant qu'une main, que d'avoir deux mains, et d'aller dans la géhenne, au feu qui ne s'éteint point, (Geenna g1067)
Où leur ver ne meurt point, et où le feu ne s'éteint point.
45 In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna g1067)
Et si ton pied te fait tomber, coupe-le; il vaut mieux pour toi que tu entres dans la vie, n'ayant qu'un pied, que d'avoir deux pieds, et d'être jeté dans la géhenne, dans le feu qui ne s'éteint point, (Geenna g1067)
Où leur ver ne meurt point, et où le feu ne s'éteint point.
47 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna g1067)
Et si ton œil te fait tomber, arrache-le; il vaut mieux pour toi que tu entres dans le royaume de Dieu, n'ayant qu'un œil, que d'avoir deux yeux, et d'être jeté dans la géhenne de feu; (Geenna g1067)
48 inda “‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’
Où leur ver ne meurt point, et où le feu ne s'éteint point.
49 Za a tsarkake kowa da wuta.
Car chacun sera salé de feu; et toute oblation sera salée de sel.
50 “Gishiri yana da daɗi, amma in ya rabu da ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da ɗanɗanonsa? Ku kasance da gishiri a cikinku, ku kuma yi zauna lafiya da juna.”
C'est une bonne chose que le sel; mais si le sel perd sa saveur, avec quoi la lui rendra-t-on? Ayez du sel en vous-mêmes, et soyez en paix entre vous.

< Markus 9 >